HomeSashen HausaBello Turji Ya Saki Mutane 32, Ya Amince Da Dakatar Da Hare-Hare...

Bello Turji Ya Saki Mutane 32, Ya Amince Da Dakatar Da Hare-Hare a Zamfara.

-

Riƙaƙƙen ɗan bindiga da aka daɗe ana nema, Bello Turji, ya saki mutane 32 da ya yi garkuwa da su, tare da amincewa da dakatar da hare-haren da ke hana manoma shiga gonaki a ƙaramar hukumar Shinkafi, ta jihar Zamfara.

Wannan na zuwa ne bayan tattaunawar sulhu da wasu malamai suka jagoranta, kamar yadda fitaccen malamin addini, Sheikh Musa Yusuf (Asadus-Sunnah), ya bayyana a wata Huɗuba da ya gabatar a Kaduna.

A cewarsa, tattaunawar ta samu ne da haɗin gwiwar al’ummar Shinkafi domin samun damar komawa gonaki cikin dajin Fakai. Taron sulhun ya gudana sau uku a watan Yuli, inda suka gana da manyan kwamandoji kamar Bello Turji, Dan Bakkolo (wanda ya ƙaryata jita-jitar mutuwarsa), Black, Kanawa da Malam Ila.

Ƴan bindigar sun miƙa wasu makamai, tare da amincewa da barin manoma su ci gaba da ayyukansu. A matsayin kyautar sulhu, Turji ya saki mutane 32 – ciki har da mata da yara, wasu daga cikinsu sun kwashe watanni a tsare, wasu kuma sun haihu a daji. Daya daga cikin su ya kamu da ciwon cizon maciji.

An kuma cimma matsaya cewa Fulani su riƙa yawo cikin yanci ba tare da fargabar farmakin sa-kai ba. Sheikh Yusuf ya ce zaman lafiya ya fara dawowa a Shinkafi sakamakon yarjejeniyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

SAKON ƘARSHEN SHEKARA NA KATSINA TIMES: Mun Fuskanci Barazana Da Kalubale A Shekarar 2025– Inji Malam Muhammad Danjuma Katsina

Tunda farko, ya yi godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki, tare da salati da aminci ga Manzon Rahama, Annabi Muhammad (SAW), iyalansa (AS) da sahabbansa (RA),...

Obi Na Shirin Shiga ADC Yayin Da Jam’iyyar Za Ta Yi Babban Taron Ta Na Ƙasa a 2026

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Labour Party (LP), Peter Obi, na dab da shiga jam’iyyar ADC, gabanin babban zaɓen shekarar 2027. Wata majiya a jam’iyyar...

Most Popular