HomeLabaraiBello Turji Ya Saki Mutane 32, Ya Amince Da Dakatar Da Hare-Hare...

Bello Turji Ya Saki Mutane 32, Ya Amince Da Dakatar Da Hare-Hare a Zamfara.

-

Riƙaƙƙen ɗan bindiga da aka daɗe ana nema, Bello Turji, ya saki mutane 32 da ya yi garkuwa da su, tare da amincewa da dakatar da hare-haren da ke hana manoma shiga gonaki a ƙaramar hukumar Shinkafi, ta jihar Zamfara.

Wannan na zuwa ne bayan tattaunawar sulhu da wasu malamai suka jagoranta, kamar yadda fitaccen malamin addini, Sheikh Musa Yusuf (Asadus-Sunnah), ya bayyana a wata Huɗuba da ya gabatar a Kaduna.

A cewarsa, tattaunawar ta samu ne da haɗin gwiwar al’ummar Shinkafi domin samun damar komawa gonaki cikin dajin Fakai. Taron sulhun ya gudana sau uku a watan Yuli, inda suka gana da manyan kwamandoji kamar Bello Turji, Dan Bakkolo (wanda ya ƙaryata jita-jitar mutuwarsa), Black, Kanawa da Malam Ila.

Ƴan bindigar sun miƙa wasu makamai, tare da amincewa da barin manoma su ci gaba da ayyukansu. A matsayin kyautar sulhu, Turji ya saki mutane 32 – ciki har da mata da yara, wasu daga cikinsu sun kwashe watanni a tsare, wasu kuma sun haihu a daji. Daya daga cikin su ya kamu da ciwon cizon maciji.

An kuma cimma matsaya cewa Fulani su riƙa yawo cikin yanci ba tare da fargabar farmakin sa-kai ba. Sheikh Yusuf ya ce zaman lafiya ya fara dawowa a Shinkafi sakamakon yarjejeniyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

NPFL Orders Barau FC vs Katsina United Clash Behind Closed Doors

The Nigeria Premier Football League (NPFL) has approved a request by Barau FC for their match against Katsina United FC to be played without fans...

Nigeria Edge Iran 2–1 in International Friendly

The Nigeria national football team, the Super Eagles, defeated Iran 2–1 in a friendly match played on Friday. The match took place at the Mardan Sport...

Most Popular