HomeSashen HausaGwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani Ya Sauya Muƙaman wasu Kwamishinoni guda...

Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani Ya Sauya Muƙaman wasu Kwamishinoni guda biyu

-

Gwamnan, ya aiwatar da wani ƙaramin sauyi a cikin Majalisar Zartaswarsa ta Jihar, inda ya sauya mukaman wasu manyan kwamishinoni guda biyu domin ƙara kuzarin aikin gwamnati jihar da inganta ayyuka ga al’ummar Jihar.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Ibraheem Musa, ya fitar a ranar Litinin.

Sanarwar ta bayyana cewa, Babban Lauyan Gwamnati kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Sule Shu’aibu (SAN), an tura shi zuwa Ma’aikatar tsaro da harkokin cikin Gida.

James Kanyip (PhD), wanda ke rike da wannan kujera a da, shi kuma zai maye gurbinsa a matsayin sabon Babban Lauyan Gwamnatin jihar da kuma Kwamishinan Shari’a.

Musa ya bayyana cewa wannan sauyin an yi shi ne domin ƙarfafa aikace-aikacen ma’aikatun ta hanyar amfani da ƙwarewar kowa ne kwamishina.

Gwamna Uba Sani ya umarci waɗannan manyan jami’an biyu da su rungumi sabbin ayyukansu a bisa gaskiya da adalci, inji sanarwar.

Gwamnan ya bayyana cikakken gamsuwar shi da ƙwarewar da kowannen su zai kawo a sabbin maƙaman nasu, yana mai cewa isar da ayyuka mai inganci shi ne ginshiƙin gwamnatin tasa.

Koda yake an bayyana sauyin a matsayin “kaɗan,” masana harkokin siyasa sun ce mukaman da aka sauya na daga cikin mafi muhimmanci da tasiri a jihar ta Kaduna, wato ɓangaren Shari’a dana tsaron cikin, waɗan da sune ke da rawar gani wajen yaki da ’yan bindigar daji, garkuwa da mutane, da kuma gyaran tsarin shari’a a jihar ta Kaduna nan.

Sule Shu’aibu, wanda lauya ne mai daraja ta SAN, ya shahara wajen jagorantar gyare-gyare a cikin tsarin shari’ar jihar Kaduna.

Matsar da shi zuwa Ma’aikatar Tsaro na Cikin gida zai sanya shi a sahun gaba wajen dai daita harkokin tsaro, musamman duba da ƙararrawar hare-haren ’yan bindiga a yankunan karkara da tashin hankali tsakanin al’ummomi.

A daya bangaren kuma, Dr. James Kanyip, masani ne a fannin shari’a da kuma tsohon Mataimakin Shugaban Ma’aikatan Gwamna, wanda ke da zurfin ilimi da ƙwarewar gudanarwa da za su taimaka masa a sabon mukaminsa a Ma’aikatar Shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina State Trains 361 Primary Healthcare Workers On Eye Care

A two-day workshop on Primary Eye Care for health personnel has commenced in Daura Senatorial District. The training, which is scheduled to run for six days...

‘Yanbindiga sun kai hari a ƙauyuka 16, sun yi ajalin mutum 5, tare da yin garkuwa da wasu da dama a jihar Zamfara.

'Yanbindigar da suka kai hari a ƙalla garuruwa 16 tsakanin Asabar da Lahadi, a ƙaramar hukumar Kaura Namoda ta jihar Zamfara, sun yi ajalin mutane...

Most Popular