HomeSashen Hausa‎Shugaban Hukumar NMDPRA Farouk Ahmed yayi Murabus Daga Mukaminsa

‎Shugaban Hukumar NMDPRA Farouk Ahmed yayi Murabus Daga Mukaminsa

-

‎Shugaban Hukumar NMDPRA, Injiniya Farouk Ahmed, ya ajiye aikinsa, lamarin da ya buɗe sabon babi a jagorancin hukumomin da ke kula da harkokin man fetur a ƙasar.

‎Farouk Ahmed na daga cikin shugabannin da aka naɗa a shekarar 2021, bayan kafuwar NMDPRA karkashin Dokar Petroleum Industry Act (PIA), wadda ta kawo sauye-sauye a tsarin kula da albarkatun man fetur da gas.

‎Murabus ɗinsa na zuwa ne a daidai lokacin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya tura sunayen sababbin shugabanni gaban Majalisar Dattawa domin tantancewa da amincewa, a ƙoƙarin da gwamnatin ke yi na ƙarfafa shugabanci da tabbatar da daidaito a muhimmin sashen makamashi.

‎A cewar Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman kan Bayanai da Dabaru, Bayo Onanuga, murabus ɗin Farouk Ahmed da na shugaban NUPRC Gbenga Komolafe ne ya ba Shugaban Ƙasa damar miƙa sunayen sababbin ƙwararru domin ci gaba da aiwatar da manufofin PIA.

‎Masu lura da harkokin makamashi na ganin wannan sauyi a matsayin wani muhimmin mataki da zai iya tasiri kai tsaye kan harkokin tace mai, rarrabawa da farashin man fetur a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎‘Yanbindiga Sun Hallaka Mutane 20, Sun Kone Rabin Wani Gari a Katsina

Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a garin Doma, dake Karamar Hukumar Faskari, dake cikin Jihar Katsina, bayan da ’yan bindiga dauke da manyan...

Jami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu– Ministan Tsaro 

Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce jami’an sojojin da aka kama bisa zargin yunkurin juyin mulki da aka dakile sun san sakamakon abin da...

Most Popular