Rahotanni da ke shigowa daga Jihar Neja na nuni da cewa wasu yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun kai wani mummunan hari a wani yanki na jihar, inda suka ƙone coci da kuma ofishin yan sanda, tare da sace wasu mutane da ba a tantance adadinsu ba.
Shaidun gani da ido sun bayyana cewa harin ya faru ne da daren jiya, lokacin da mazauna yankin ke tsaka da harkokinsu na yau da kullum. Ƴan bindigar sun shigo garin ne a kan babura, suka fara harbe-harbe domin tsoratar da jama’a kafin su banka wa coci da ofishin ƴan sanda wuta.
Wani mazaunin yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce lamarin ya jefa jama’a cikin firgici da tashin hankali. Ya ƙara da cewa bayan lalata kadarorin gwamnati da na addini, yan bindigar sun yi awon gaba da wasu mutane, ciki har da mata da matasa.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, jami’an tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan adadin mutanen da aka sace ko asarar rayuka ba. Sai dai an tabbatar da cewa dakarun tsaro sun fara sintiri a yankin domin farautar masu laifin da kuma ƙoƙarin ceto waɗanda aka sace.
Gwamnatin Jihar Neja ta yi Allah-wadai da harin, tare da tabbatar wa al’umma cewa za ta ɗauki tsauraran matakai domin dawo da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
Ana ci gaba da sa ido kan lamarin yayin da ake sa ran ƙarin bayani daga hukumomin tsaro.
