HomeSashen HausaWest Ham Za Ta Siyar Da Mohammed Kudus Don Ɗauko Ademola Lookman

West Ham Za Ta Siyar Da Mohammed Kudus Don Ɗauko Ademola Lookman

-

Ƙungiyar ƙwallon kafa ta West Ham United da ke buga gasar Premier League a Ingila na shirin siyar da ɗan wasanta Mohammed Kudus domin samun damar ɗauko ɗan wasan gaba na Najeriya, Ademola Lookman.

Rahotanni daga kafafen wasanni na Ingila na nuna cewa West Ham tana duba yiwuwar rabuwa da Kudus, wanda ƙungiyar ta sayo daga Ajax ta ƙasar Netherlands a bara, domin ƙarfafa ɓangaren gaba da Ademola Lookman, wanda ke taka rawar gani a Atalanta ta Italiya.

Lookman yayi fice a kakar da ta gabata, musamman bayan da ya jefa ƙwallaye uku (hat-trick) a gasar Europa League da ta tabbatar wa Atalanta samun kambun zakara. Wannan bajinta na daga cikin ababen da suka jawo hankalin West Ham da wasu manyan ƙungiyoyi a Turai.

Idan har West Ham ta cimma matsaya da Atalanta da kuma wakilan Lookman, to akwai yiyuwar ganin ɗan wasan na Najeriya ya koma London kafin kakar 2025/2026 ta fara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Hadiza Gabon Na Shirin Barin Kaduna Zuwa Kano Da Shirin Talk Show

Daya daga cikin makusantar tsohuwar Jarumar Kanywood Hadiza Gabon, ya tabbatar wa Jaridar ALFIJIR NEWS, wanda a yanzu jarumar ta fara tinanin dauke zauren Shirin...

Sojoji Sun Ceto Mutune 7 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Tsanyawa, Jihar Kano

Sojojin Operation MESA da suka haɗa da jami’an Birgediya ta 3 ta rundunar sojin Najeriya, sojojin saman Najeriya da kuma ’yansanda sun ceto mutune bakwai...

Most Popular