HomeSashen HausaMagoya Bayan APC Da Dama Sun Sauya Sheƙa Zuwa ADC a Jihar...

Magoya Bayan APC Da Dama Sun Sauya Sheƙa Zuwa ADC a Jihar Sokoto

-

A Jihar Sokoto, magoya bayan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da dama, musamman daga Ƙaramar Hukumar Gada, sun sauya sheƙa zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Rahotanni daga majiyoyi mai tushe sun tabbatar da cewa waɗanda suka sauya sheƙar sun yi hakan ne saboda ƙorafin rashin tsaro, talauci, da kuma gazawar gwamnati wajen samar da ingantaccen shugabanci.

Tsohon Sanata, Abubakar Gada, wanda ya karɓi sabbin ‘yan jam’iyyar ADC, ya bayyana cewa jama’a na neman mafita daga halin da ake ciki, inda ya jaddada cewa ADC na da shirin siyasa mai ma’ana wanda zai iya kawo sauyi a rayuwar al’umma.

Inda ya ƙara da cewa:
“Mutane sun gaji da talauci da rashin aikin yi. Suna so su ga shugabanci na gaskiya da tsari mai inganci, shi ya sa suka yo dandazo zuwa ADC.”

Binciken jaridu irin su Punch Newspapers, Daily Post Nigeria, da Leadership ya nuna cewa wannan sauyin sheƙa na iya ƙara ƙarfafa ADC a Sokoto, tare da yiwuwar yin tasiri a siyasar jihar a zaben dake gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular