HomeSashen HausaDalilan Da Suka Sanya Shugaba Tinubu Ya Yanke Hutunsa Kafin Wa'adi- Rahoton...

Dalilan Da Suka Sanya Shugaba Tinubu Ya Yanke Hutunsa Kafin Wa’adi- Rahoton Daily Trust

-

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya dakatar da hutun da yake yi a ƙasashen waje, inda ya dawo Abuja ranar Talata domin ci gaba da gudanar da manyan ayyukan gwamnati.

Wani rahoto da jaridar Daily Trust ta wallafa ya bayyana cewa babban dalilin dawowar shugaban shine ƙarewar wa’adin dokar gaggawa a Jihar Rivers, wanda ya bukaci kulawarsa kai tsaye kan batutuwan tsaro da siyasa da suka taso a jihar.

Baya ga haka, rahoton ya ƙara da cewa shugaba Tinubu na bukatar gudanar shirye-shirye domin halartar babban taron Majalisar Dinkin Duniya (UNGA) karo na 80 da zai gudana a birnin New York nan da makonni masu zuwa.

Ko da yake fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da cewa duk da cewa hutun nasa “na aiki” ne, inda yake ci gaba da kula da al’amuran gwamnati daga wajen ƙasa, akwai wasu batutuwan cikin gida da suka bukaci kasancewarsa a Abuja domin daukar matakai na kai tsaye.

Tuni dai masu goyon bayan gwamnati suka yaba da matakin shugaban, suna cewa hakan ya nuna jajircewarsa wajen fifita al’amuran ƙasa akan hutun kansa. Sai dai wasu ‘yan adawa sun yi nuni da cewa dawowar nan ta nuna irin gibin da ke akwai a wajen tsarin dake cikin gwamnatin, inda suka yi kira da a ƙarfafa tsarin gudanarwa wanda ba zai tsaya kan kasancewar shugaban kai tsaye ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Abinda Ya Faru Da Ni Ya Zame Min Alkhairi– Malam Bala Dorayi

Malam Bala Dorayi, wanda aka fi sani da Sarkin Yakin Karyar Ƙasar Hausa, ya bayyana cewa abin da ya faru da shi a baya kaddara...

‎Kim Jong Un Ya Zaɓi Ƴarsa Mai Shekara 13 a Matsayin Wadda Za Ta Gaje Shi ‎

Rahotanni daga National Intelligence Service (NIS) sun bayyana cewa shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong Un, ya zaɓi ƴarsa mai shekara 13, Kim Ju Ae,...

Most Popular