HomeSashen HausaDA ƊUMI-ƊUMI: Soja AM Yerima Ya Tsallake Rijiya Da Baya Yau A...

DA ƊUMI-ƊUMI: Soja AM Yerima Ya Tsallake Rijiya Da Baya Yau A Abuja

-

Wani matashin jami’in Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, Lt. A.M. Yarima, wanda ya yi rashin jituwa kwanan nan da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya kubuta daga yunkurin kisan gilla da aka yi masa da yammacin Lahadi.

 

Majiyoyin soja sun shaida wa Vanguard cewa wasu mutane da ba a san ko su waye ba, sanye da baƙaƙen kaya, suna cikin manyan motoci biyu kirar Hilux marasa lambar rajista, sun bi sawun Yarima. Ana zargin motocin sun bi shi daga tashar mai ta NIPCO da ke kusa da Line Expressway zuwa Gado Nasco Way.

 

A cewar majiyar, jami’in ya lura ana bin sawunsa, sai ya aiwatar da wata dabara ta dabarun tsaro, inda ya samu ya tsere wa waɗanda ake zargin ‘yan harin ne. Lamarin ya faru ne kimanin ƙarfe 6:30 na yamma.

 

Majiyar ta ƙara da cewa ana bincike kan lamarin, kuma ana daukar shi da muhimmanci yadda ya dace, tare da ƙarin bayanai da aka ɓoye domin kada a kawo cikas ga binciken.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kwankwaso Na Nazarin Hada Kai da Atiku da Obi Domin Shiga ADC

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Jagoran New Nigeria People’s Party (NNPP), Sen Rabiu Musa Kwankwaso, na nazarin yiwuwar haɗa kai da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa...

Katsina Za Ta Karɓi Baƙuncin Mauludin Ƙasa na Inyass karo na Uku a Janairu 2026

An bukaci Gidan Rediyon Jihar Katsina da ya bayar da cikakken hadin kai da goyon baya wajen watsa dukkan ayyukan Mauludin Ƙasa na Inyass na...

Most Popular