HomeSashen HausaNajeriya Za Ta Ɗauki Sabbin Sojoji Dubu 24, Domin Inganta Tsoron Ƙasar

Najeriya Za Ta Ɗauki Sabbin Sojoji Dubu 24, Domin Inganta Tsoron Ƙasar

-

Babban Hafsan Sojojin Najeriya (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayyana shirin daukar sabbin sojoji 24,000 domin kara karfin rundunar sojin kasar a yaki da matsalolin tsaro.

 

Janar Shaibu ya sanar da hakan ne a Kaduna yayin ziyarar aiki da ya kai Runduna ta 1, inda ya ce sabbin cibiyoyin horaswa guda uku—da Shugaba Bola Tinubu ya amince da su—za su samar da sojojin da suka kware a sabon dabarun yaki da horo na zamani.

 

Ya ce rundunar na fatan horas da sojoji 12,000 cikin watanni shida, kuma idan an gudanar da horaswa a matakai biyu za a iya samar da jimillar dakarun 24,000.

 

Babban hafsan ya jaddada cewa shirin ba wai kara yawan sojoji ba ne kawai, har ma da tabbatar da inganci, kwarewa, da shirin tunkarar barazanar tsaro da ke kara kamari a fadin kasar nan.

 

Ya kuma tabbatar da kudirin rundunar wajen inganta jin dadin ma’aikata a karkashin manufar “Soja Na Farko”.

 

Ana sa ran sabbin dakarun za su karfafa martanin sojoji, kare al’umma, da kuma inganta tsaro a manyan yankunan da ake fama da rikice-rikice.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

An Zaɓi Hon. Dauda Kurfi A Matsayin Shugaban Ƙungiyar Tsofaffin Kansiloli A Jihar Katsina

Tsofaffin Kansiloli, sun rushe shugabancin ƙungiyar tsofaffin Kansilolin ta ƙasa reshen jihar Katsina, inda suka zaɓi Hon. Dauda Kurfi, a matsayin shugaban ƙungiyar tsofaffin Kansiloli...

Dikko Radda Ya Amince Da Naɗin Sabbin Manyan Sakatarori a Jihar Katsina

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya amince da naɗin sabbin manyan sakatarorin jihar.   Gwamnan ya ce an gudanar da naɗin bi sa cancanta da...

Most Popular