HomeSashen HausaNajeriya Za Ta Ɗauki Sabbin Sojoji Dubu 24, Domin Inganta Tsoron Ƙasar

Najeriya Za Ta Ɗauki Sabbin Sojoji Dubu 24, Domin Inganta Tsoron Ƙasar

-

Babban Hafsan Sojojin Najeriya (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayyana shirin daukar sabbin sojoji 24,000 domin kara karfin rundunar sojin kasar a yaki da matsalolin tsaro.

 

Janar Shaibu ya sanar da hakan ne a Kaduna yayin ziyarar aiki da ya kai Runduna ta 1, inda ya ce sabbin cibiyoyin horaswa guda uku—da Shugaba Bola Tinubu ya amince da su—za su samar da sojojin da suka kware a sabon dabarun yaki da horo na zamani.

 

Ya ce rundunar na fatan horas da sojoji 12,000 cikin watanni shida, kuma idan an gudanar da horaswa a matakai biyu za a iya samar da jimillar dakarun 24,000.

 

Babban hafsan ya jaddada cewa shirin ba wai kara yawan sojoji ba ne kawai, har ma da tabbatar da inganci, kwarewa, da shirin tunkarar barazanar tsaro da ke kara kamari a fadin kasar nan.

 

Ya kuma tabbatar da kudirin rundunar wajen inganta jin dadin ma’aikata a karkashin manufar “Soja Na Farko”.

 

Ana sa ran sabbin dakarun za su karfafa martanin sojoji, kare al’umma, da kuma inganta tsaro a manyan yankunan da ake fama da rikice-rikice.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎Katsina Judiciary Trains Magistrates on ICT, AI and New Media

The Katsina State Judiciary on Tuesday organised a specialised capacity-building workshop for magistrates aimed at strengthening the justice system in the digital age. ‎The workshop, themed...

Alƙalin Alƙalai na Jihar Katsina Ya Ƙaddamar Da Bada Horo Ga Alƙalai Kan Ilimin (AI) da Kafofin Yaɗa Labarai Na Zamani

Babbar Kotun Shari’a ta Jihar Katsina ta shirya wani taron horaswa na musamman ga alƙalan majistire, domin ƙarfafa tsarin shari’a daidai da buƙatun zamani. Taron wanda...

Most Popular