HomeSashen HausaDuniya Za Ta Fuskanci Ƙalubale, Idan Najeriya Ta Wargaje– Inji Sanata Kashim...

Duniya Za Ta Fuskanci Ƙalubale, Idan Najeriya Ta Wargaje– Inji Sanata Kashim Shettima

-

Mataimakin Shugaban Ƙasa a Najeriya, Kashim Shettima ya ce gwamnatin Tinubu ba za ta taɓa bari Najeriya ta ruguje a hannunta ba, komai rintsi.

 

Kamar yadda Nigerian Post ta samu daga Aminiya, Shettima ya faɗi haka ne yayin da yake jawabi a wajen yaye ɗaliban Cibiyar Nazarin Manufofi da Muhimman Buƙatu ta Ƙasa (NIPSS) da ke Kuru a Jihar Filato.

 

Ya ƙara da cewa idan har Najeriya ta tarwatse to ’yan ƙasar, sama da mutum miliyan 50 za su fantsama su tsallaka Turai.

 

Don haka ya ce zai fi zama alheri ga duniya idan Najeriya ta ɗore a matsayin ƙasa guda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎‘Yanbindiga Sun Hallaka Mutane 20, Sun Kone Rabin Wani Gari a Katsina

Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a garin Doma, dake Karamar Hukumar Faskari, dake cikin Jihar Katsina, bayan da ’yan bindiga dauke da manyan...

Jami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu– Ministan Tsaro 

Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce jami’an sojojin da aka kama bisa zargin yunkurin juyin mulki da aka dakile sun san sakamakon abin da...

Most Popular