HomeSashen HausaNijeriya Ta Musanta Zargin Leken Asiri Kan Jirginta Da Ke Burkina-Faso

Nijeriya Ta Musanta Zargin Leken Asiri Kan Jirginta Da Ke Burkina-Faso

-

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da ke cewa jirginta kirar C-130 da ya sauka ba tare da shiri ba a Bobo-Dioulasso, Burkina Faso, ya je aikin leken asiri a boye.

 

Runudunar ta ce rahoton karya ne kuma ba shi da tushe, tana mai jaddada cewa jirgin na kan hanyarsa ta zuwa Portugal domin gyara, kuma saukar gaggawar da ya yi ta faru ne saboda dalilan tsaro bisa ka’idojin sufurin jiragen sama na duniya.

 

Bayanai da Jaridar The Nation sun ce wata majiya a hedkwatar tsaron NAF ta ce jirgin yana dauke da dukkan takardun izini, kuma an bi dukkan matakan da doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular