HomeSashen Hausa‎Gwamnan Gombe Ya Kori Wasu hadimansa Huɗu Kan Zargin Cin Zarafin Kansila

‎Gwamnan Gombe Ya Kori Wasu hadimansa Huɗu Kan Zargin Cin Zarafin Kansila

-

Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya kori wasu hadimansa huɗu daga aiki nan take, bayan an same su da laifin cin zarafin wani kansila mai ci, Abdulrahman Abubakar Sharif, mai wakiltar yankin Shamaki a ƙaramar hukumar Gombe.

‎Matakin ya biyo bayan rahoton kwamitin bincike da bayanan jami’an tsaro, kamar yadda Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ya bayyana.

‎Waɗanda aka kora sun haɗa da Adamu Abdullahi Danko, Garba Mohammed Mai Rago, Rabiu Suleman Abubakar da Alhaji Ibrahim Baban Kaya, dukkaninsu Mataimaka ne na Musamman (SAS II) a fannoni daban-daban.

‎Gwamnatin jihar ta umurce su da su miƙa dukkan kayayyakin gwamnati da ke hannunsu nan take.

‎A sanarwar da Babban Daraktan Yaɗa Labarai, Ismaila Uba Misilli, ya fitar, gwamnatin ta jaddada cewa ba za ta lamunci cin zarafi ba, tare da ci gaba da kare doka, adalci da zaman lafiya a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎Gwamnan Plateau Ya Kaddamar Da Jami,’an Tsaro 1,450 Na Operation Rainbow

Gwamnan Jihar Plateau, Barrista Caleb Manasseh Mutfwang, a ranar Talata ya kaddamar da jami'an tsaro 1,450 da aka kammala horaswa a karkashin shirin Operation Rainbow,...

‎APC Ta Shirya Karɓar Gwamnan Plateau a Wata Mai Zuwa

‎Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta tabbatar da shirinta na karɓar Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Mutfwang, a wata mai zuwa, lamarin da ya fara jawo...

Most Popular