HomeSashen Hausa‎Ɗan Jihar Katsina Ya Sami Mukami Mai Girma a Hukumar NDLEA

‎Ɗan Jihar Katsina Ya Sami Mukami Mai Girma a Hukumar NDLEA

-

Wani ɗan asalin jihar Katsina, Ahmed Idris Zakari, ya sami ƙarin girma a Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), inda aka naɗa shi zuwa mukamin Assistant Commander General of NDLEA, wani mukami dake daf da na ƙarshe a tsarin shugabancin hukumar.

Ahmed Idris Zakari, wanda ya fito daga ƙaramar hukumar Katsina, ya samu wannan matsayi ne sakamakon jajircewarsa, kwarewa da kuma gudummawar da ya bayar tsawon shekarun da ya shafe yana aiki a hukumar, musamman a fannin yaƙi da miyagun ƙwayoyi da kare lafiyar al’umma.

Masu ruwa da tsaki da dama sun bayyana wannan cigaba a matsayin abin alfahari ga jihar Katsina dama Arewa gaba ɗaya, inda suka yaba da yadda ƴayan jihar ke cigaba da samun manyan mukamai a hukumomin ƙasa.

An yi addu’ar Allah Ya sanya alheri a wannan ƙarin girma, Ya kuma ba shi ikon sauke nauyin da aka ɗora masa cikin adalci da gaskiya, tare da cigaba da bada gudummawa wajen yaƙi da miyagun ƙwayoyi a Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎Kwankwaso Ya Bayyana Wadanda Zasu Yi Takarar Zaben Cike Gurbi A Jam’iyyar NNPP

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya amince da bai wa ’ya’yan ’yan Majalisar Jiha biyu da suka rasu, damar tsayawa takara, domin neman...

‎Gwamnatin Tarayya ta Kammala Horas da Sama da Jami’an Tsaron Daji 7,000 a Jihohi 7

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ce ta kammala horas da sama da sabbin jami’an tsaron daji 7,000 da aka dauka aiki daga jihohi bakwai, a wani...

Most Popular