HomeSashen HausaJiragen Yaƙin Da Muka Siya Daga Amurka, Za Su Iso Najeriya Nan...

Jiragen Yaƙin Da Muka Siya Daga Amurka, Za Su Iso Najeriya Nan Bada Jimawa Ba- Tinubu

-

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta yi odar jiragen yaƙi guda huɗu daga Amurka, waɗanda za su iso Najeriya nan ba da jimawa ba, domin ƙara ƙarfafa yaƙi da rashin tsaro da ta’addanci.

 

Tinubu ya bayyana hakan ne a yayin ganawarsa da tawagar kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) a gidansa da ke Lagos.

 

Ya ce duk da jinkirin isowar jiragen, gwamnati na ci gaba da neman taimako daga ƙasashen waje, ciki har da Turkiyya.

 

Wannan na zuwa ne bayan Amurka ta kai hare-haren sama kan ‘yan ta’adda a Arewa maso yammacin Najeriya, lamarin da gwamnatin Najeriya ta tabbatar, tana mai cewa an yi shi ne bisa haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.

 

Shugaban ƙasar ya kuma tabbatar da cewa shirin kafa ‘yansandan al’umma da na jiha zai zama gaskiya da zarar majalisar dokoki ta Kasa ta kammala gyare-gyaren dokokin da suka dace.

 

Tinubu ya jaddada cewa gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen dawo da zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziki a ƙasar, duk da ƙalubalen tsaro da ake fuskanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Afenifere Ta Goyi Bayan Harin Da Amurka Ta Kai a Sokoto

Kungiyar Afenifere, wadda ke wakiltar al’ummar Yarbawa a fannin siyasa da zamantakewa, ta bayyana goyon bayanta ga hare-haren jiragen yakin Amurka da aka kai kan...

‎Majalisar Wakilai Ta Umarci A Yi Gyare-gyare a Kundin Sabbin Dokokin Haraji Bayan Samun Kura-kurai

Majalisar Wakilai ta bayar da umarnin sake duba sabbin dokokin gyaran haraji da aka amince da su kwanan nan, biyo bayan zargin bambance-bambance tsakanin dokokin...

Most Popular