HomeSashen HausaYaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

-

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe mai gidansa, Abdul’aziz Aliyu Dan Malam, ta hanyar caka masa almakashi.

‎Majiyar Reality TV news ta ruwaito cewa lamarin ya auku ne da yammacin Asabar, 17 ga watan Janairu, 2026, da misalin karfe 5:40 na yamma, a lokacin da marigayin ya kulle shagonsa bayan kammala harkokin kasuwanci, yana kan hanyarsa ta komawa gida tare da mahaifiyarsa.

‎Bayanai daga majiyoyi na kusa da iyalan marigayin sun ce an samu cacar baki ne tsakanin marigayin da wasu daga cikin yaran shagon, sakamakon zargin sata, lamarin da daga bisani ya rikide zuwa tashin hankali. A dalilin rikicin ne, daya daga cikin yaran shagon ya caka masa almakashi a gaban mahaifiyarsa.
‎Inda aka garzaya da marigayin zuwa Asibitin Koyarwa ta Tarayya (FTH) Gombe, inda jami’an lafiya suka tabbatar da rasuwarsa.

‎Rahotanni sun kuma nuna cewa marigayin sabon ango ne, kasancewar an daura aurensa ne a 26 ga watan Disamba, 2025, makonni uku kacal kafin faruwar wannan lamari.

‎An dai shirya gudanar da sallar jana’izar marigayin da misalin karfe 11 na safiyar Lahadin yau a Masallacin Juma’a na Bolari, dake birnin Gombe.

‎Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da cikakken bayani kan matakin da aka dauka ba, yayin da jama’a ke ci gaba da fatan ganin an gudanar da bincike tare da ɗaukar matakin da ya dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

‎’Yan Garin Dutsinma Sun Nuna Farin Ciki Bayan Zaman Sulhu da Barayin Daji

Al’ummar garin Dutsinma dake Jihar Katsina sun bayyana matuƙar farin ciki da jin daɗi biyo bayan zaman sulhun da aka kulla tsakanin jama’ar garuruwan dake...

Most Popular