HomeLabarai‎Shelkwatar Tsaro Ta Musanta Yin Watsi Da Sojojin Da Suka Jikkata a...

‎Shelkwatar Tsaro Ta Musanta Yin Watsi Da Sojojin Da Suka Jikkata a Fagen-daga ‎

-

Hedikwatar tsaro ta ƙasa ta ƙaryata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ake zargin cewa tana yin watsi da sojojin da suka jikkata yayin aiki.

‎Shelkwatar tsaron ta bayyana cewa, sabanin wani bidiyo da ya yaɗu wanda ke zargin “rashin kulawa da halin ko-in-kula ga walwalar sojojin da suka jikkata a bakin aiki,” walwalar jami’anta, musamman waɗanda suka samu raunuka yayin aiki, na daga cikin manyan abubuwan da take ba muhimmanci.

‎A cewar wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Samaila Uba, ya fitar ranar Talata, dukkan sojojin da suka jikkata a yayin ayyuka ko fagen fama suna da haƙƙin samun cikakken kulawar lafiya, a cikin gida ko a ƙasashen waje, gwargwadon nau’i da tsananin raunukan da suka samu, bisa ƙa’idojin kiwon lafiya da sojojin Najeriya suka tanada.

‎Sanarwar ta ce: ‎”Sojojin Najeriya na ba da damar samun kulawa ta musamman ga waɗanda suka jikkata sosai a wuraren kiwon lafiya ko a ƙasashen waje idan irin wannan kulawar ta zama wajibi.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular