HomeSashen Hausa‎Shelkwatar Tsaro Ta Musanta Yin Watsi Da Sojojin Da Suka Jikkata a...

‎Shelkwatar Tsaro Ta Musanta Yin Watsi Da Sojojin Da Suka Jikkata a Fagen-daga ‎

-

Hedikwatar tsaro ta ƙasa ta ƙaryata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ake zargin cewa tana yin watsi da sojojin da suka jikkata yayin aiki.

‎Shelkwatar tsaron ta bayyana cewa, sabanin wani bidiyo da ya yaɗu wanda ke zargin “rashin kulawa da halin ko-in-kula ga walwalar sojojin da suka jikkata a bakin aiki,” walwalar jami’anta, musamman waɗanda suka samu raunuka yayin aiki, na daga cikin manyan abubuwan da take ba muhimmanci.

‎A cewar wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Samaila Uba, ya fitar ranar Talata, dukkan sojojin da suka jikkata a yayin ayyuka ko fagen fama suna da haƙƙin samun cikakken kulawar lafiya, a cikin gida ko a ƙasashen waje, gwargwadon nau’i da tsananin raunukan da suka samu, bisa ƙa’idojin kiwon lafiya da sojojin Najeriya suka tanada.

‎Sanarwar ta ce: ‎”Sojojin Najeriya na ba da damar samun kulawa ta musamman ga waɗanda suka jikkata sosai a wuraren kiwon lafiya ko a ƙasashen waje idan irin wannan kulawar ta zama wajibi.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

‎Ganduje Ba Shi da Alhakin Sace Dadiyata – Shehu Sani

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta 8, Shehu Sani, ya karyata zargin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna,...

Most Popular