HomeSashen HausaShugaban Rundunar Horaswa ta Sojin Sama Ya Kai Ziyara Kainji, Ya Jaddada...

Shugaban Rundunar Horaswa ta Sojin Sama Ya Kai Ziyara Kainji, Ya Jaddada Shirye-shiryen Murƙushe ‘Yan Ta’adda

-

Shugaban rundunar horaswa ta Sojin Sama ta Nijeriya, Air Vice Marshal Esen Paul Efanga, ya kai ziyara sansanin Sojin Sama na Kainji domin duba

‎shirye-shiryen aiki da ƙarfinsu wajen yaƙi da ƴan ta’adda a sassan ƙasar nan.

‎A yayin ziyarar, Efanga ya yabawa jami’ai bisa ƙwazo da jajircewa, tare da nuna gamsuwa da yadda jiragen sama ke gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

‎Ya jaddada cewa Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya na ci gaba da samun rinjaye a sararin samaniya, tare da cikakken shiri na kai farmaki a kowane lokaci.

‎Shugaban rundunar ya kuma tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa Sojin Sama na da cikakken iko da ƙarfin kare martabar ƙasa, inda ya ce ba za a sassauta ba wajen ci gaba da kai hare-hare cikin ƙarfi da daidaito har sai an samu tsaro mai ɗorewa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

An Kama Tsohon Abokin Ganduje Yayin Da Yake Shirin Barin Kano

Jami’an Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano sun kama wani muhimmin mutum da ake zargi da badakalar mallakar Dala Inland Dry Port—wani shiri na biliyoyin nairori—a...

Ba Da Jimawa Ba Za Mu Kawo Ƙarshen Rikicin Masarautar Kano– Gwamnatin Kano

Gwamnatin jihar Kano ta ce nan ba jimawa ba za ta kawo karshen rikicin da ya daɗe yana faruwa kan masarautar Kano, inda mutum biyu...

Most Popular