HomeSashen HausaShugaban Rundunar Horaswa ta Sojin Sama Ya Kai Ziyara Kainji, Ya Jaddada...

Shugaban Rundunar Horaswa ta Sojin Sama Ya Kai Ziyara Kainji, Ya Jaddada Shirye-shiryen Murƙushe ‘Yan Ta’adda

-

Shugaban rundunar horaswa ta Sojin Sama ta Nijeriya, Air Vice Marshal Esen Paul Efanga, ya kai ziyara sansanin Sojin Sama na Kainji domin duba

‎shirye-shiryen aiki da ƙarfinsu wajen yaƙi da ƴan ta’adda a sassan ƙasar nan.

‎A yayin ziyarar, Efanga ya yabawa jami’ai bisa ƙwazo da jajircewa, tare da nuna gamsuwa da yadda jiragen sama ke gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

‎Ya jaddada cewa Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya na ci gaba da samun rinjaye a sararin samaniya, tare da cikakken shiri na kai farmaki a kowane lokaci.

‎Shugaban rundunar ya kuma tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa Sojin Sama na da cikakken iko da ƙarfin kare martabar ƙasa, inda ya ce ba za a sassauta ba wajen ci gaba da kai hare-hare cikin ƙarfi da daidaito har sai an samu tsaro mai ɗorewa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Kanwan Katsina Advocates Establishment of FM Stations Across 3 Senatorial Zones Katsina

The Kanwan Katsina District Head of Ketare, Alhaji Usman Bello Kankara mni, has emphasized the need for continuous training and capacity building for journalists, particularly...

‎Ganduje Ba Shi da Alhakin Sace Dadiyata – Shehu Sani

Tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Tsakiya a Majalisar Dattawa ta 8, Shehu Sani, ya karyata zargin da tsohon gwamnan Jihar Kaduna,...

Most Popular