Gwamnatin Jihar Katsina ta ce ta kammala biyan albashin ma’aikatanta na watan Janairu, duk da raguwar kuɗaɗen da jihar ta samu daga Asusun Tarayya (FAAC).
Rahoton jaridar Punch da aka wallafa a ranar Alhamis, 6 ga watan Fabrairu, 2026, ya bayyana cewa matakin ya zo ne a daidai lokacin da jihohi da dama ke fuskantar ƙalubalen kuɗi sakamakon raguwar kuɗin da ake rabawa daga gwamnatin tarayya.
A cewar rahoton, gwamnatin Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa ta ba da fifiko ga biyan albashi da sauran muhimman ayyuka, domin kare walwalar ma’aikata da kauce wa tsaiko a harkokin mulki.
Masu sharhi kan tattalin arziƙi na ganin cewa biyan albashin duk da raguwar FAAC na nuna tsauraran matakan tsima da tanadi da kuma yadda gwamnatin jihar ke ƙoƙarin daidaita kasafin kuɗinta a wannan yanayi na matsin tattalin arziƙi.
