Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ba ta haramta wasan ƙwallo gaba ɗaya a watan Ramadan ba, sai dai ta ɗauki matakin hana yin wasan da daddare a kan tituna da kuma wuraren da ke haddasa cunkoso da kawo cikas ga zirga-zirga.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Jami’in Sashen Fasahar Sadarwa na Hisbah a Dandume, Malam Bin Haris, ya fitar domin fayyace matsayar hukumar ga al’umma.
A cewar sanarwar, an takaita wasan ƙwallo da daddare ne musamman a wuraren da ke kawo tangarda ga zirga-zirgar ababen hawa, da kuma a lokutan da jama’a ke tafiya masallatai domin gudanar da ibadu a watan Ramadan. Hukumar ta ce matakin na da nufin kare lafiyar al’umma, tabbatar da tsaro, da samar da kwanciyar hankali a wannan wata mai alfarma.
Haka kuma, hukumar ta yi kira ga al’umma da su guji yaɗa jita-jita ko karkatar da bayani dangane da umarninta, tare da bin doka, mutunta hanyoyi, da kuma bada haɗin kai ga jami’an tsaro domin samun zaman lafiya da nutsuwa a duk tsawon watan Ramadan.
Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina ta jaddada cewa ƙoƙarinta na ci gaba da kasancewa ne wajen gyara al’umma da kare martabar addini ba tare da tauye hakkokin jama’a ba.
