HomeLabaraiKotu Ta Tsare Shugaban KANSIEC da Wasu Mutum 2 Kan Zargin Badaƙalar...

Kotu Ta Tsare Shugaban KANSIEC da Wasu Mutum 2 Kan Zargin Badaƙalar Kuɗaɗe

-

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin tsare Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Kano (KANSIEC), Sani Malumfashi, tare da Sakataren hukumar, Anas Muhammed Mustapha, da Ado Garba, Mataimakin Darakta, bisa zargin aikata badakalar kuɗi da ta kai Naira biliyan ɗaya.

‎Mai shari’a James Omotosho ne ya bayar da umarnin tsare su a gidan gyaran hali na Kuje, Abuja, bayan da waɗanda ake tuhumar suka musanta laifuka guda shida da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta tuhume su da aikatawa.

‎A cewar ICPC, ana zargin jami’an da karɓar kuɗaɗe har Naira miliyan 450, Naira miliyan 310 da kuma Naira miliyan 260 ba bisa ƙa’ida ba, a tsakanin watan Nuwamba da Disamba na shekarar 2024, kuɗaɗen da aka ce sun sabawa doka.

‎Kotun ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 28 ga Janairu, domin duba buƙatar belin waɗanda ake tuhuma, yayin da ake ci gaba da bincike kan zargin da ake musu.

Nigerian Post ta bibiyi cewa, ‎lamarin dai ya ja hankalin jama’a, musamman ganin muhimmancin hukumar KANSIEC a tsarin dimokuraɗiyya da gudanar da sahihin zaɓe a Jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular