HomeSashen HausaAn Kama Tsohon Abokin Ganduje Yayin Da Yake Shirin Barin Kano

An Kama Tsohon Abokin Ganduje Yayin Da Yake Shirin Barin Kano

-

Jami’an Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano sun kama wani muhimmin mutum da ake zargi da badakalar mallakar Dala Inland Dry Port—wani shiri na biliyoyin nairori—a daidai lokacin da yake shirin barin jihar Kano ta jirgin sama.

 

An kama Ahmad Rabiu, tsohon Darakta Janar (Managing Director) na tashar jiragen ruwa ta tsandauri (Dry Port), kuma tsohon Kwamishinan Kasuwanci a Jihar Kano, ne a ranar Laraba a Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano, kamar yadda majiyoyi daga rundunar ’yan sanda suka tabbatar.

 

Rahotanni sun nuna cewa kama Rabiu na da alaka da zargin damfara da rikicin mallaka da ke tattare da Dala Inland Dry Port—lamarin da ya jawo cece-kuce a fagen siyasa da kasuwanci, inda ake alakanta shi da wasu manyan jiga-jigan gwamnati a baya, ciki har da tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

 

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ba ta fitar da cikakken bayani kan tuhume-tuhumen da ake yi wa Rabiu ba. Sai dai majiyoyi sun ce ana ci gaba da bincike, kuma ana sa ran za a gurfanar da shi gaban kotu idan binciken ya kammala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ba Da Jimawa Ba Za Mu Kawo Ƙarshen Rikicin Masarautar Kano– Gwamnatin Kano

Gwamnatin jihar Kano ta ce nan ba jimawa ba za ta kawo karshen rikicin da ya daɗe yana faruwa kan masarautar Kano, inda mutum biyu...

Gwamnan Kano Da Muƙarrabansa Za Su Yi Nadamar Barinmu Nan Gaba– Inji Kwankwaso

Jagoran jam’iyyar NNPP na Ƙasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, tare da muƙarrabansa za su yi nadamar barin...

Most Popular