HomeSashen HausaGwamnatin Kano ta biya wa fursunoni 58 sun zana jarabawar NECO ta...

Gwamnatin Kano ta biya wa fursunoni 58 sun zana jarabawar NECO ta 2025

-

A wani muhimmin mataki na gyaran hali da rayuwar ɗaurarru, fursunoni 58 a jihar Kano ne su ka zana jarabawar kammala makarantar sakandire ta kasa, NECO ta 2025.

Hukumar Kula da gidajen gyaran hali ta Najeriya, reshen jihar Kano ce ta sanar da hakan a cikin wata sanarwa a yau Litinin, inda ta bayyana wannan ci gaba a matsayin babban nasara wajen kokarin gyara da mayar da fursunoni cikin al’umma.

A cewar sanarwar da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Musbahu Lawan K/Nasarawa, ya sanya wa hannu, wannan nasara ta samu ne sakamakon goyon bayan gwamnatin jihar Kano wadda ta biya kuɗin rajistar dukkan fursunonin da suke zana jarabawar.

“Goyon bayan da mai girma Gwamna, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya bayar ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da jin daɗi, gyaran hali da kuma sake shigar da fursunoni cikin al’umma,” inji sanarwar.

Hukumar ta bayyana godiyarta ga Gwamna Yusuf saboda “goyon bayan sa mara yankewa da haɗin kai,” tana mai cewa wannan taimako zai karfafa gwiwar fursunonin tare da ba su wata dama ta biyu wajen samun ilimi da kyakkyawar makoma.

“Hukumar Kula da Fursunoni ta Najeriya, reshen jihar Kano, za ta ci gaba da tabbatar da yanayi mai kyau na gyaran hali da tarbiyya ga fursunoni, kuma muna alfahari da samun goyon bayan gwamnatin jihar Kano wajen wannan kokari,” inji sanarwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‘Yan Bindigar Da Suka Sace Mutane 3 A Tsakiyar Katsina Sun Nemi Miliyan 600 Kuɗin Fansa

Wasu ’yan bindiga da suka sace wasu ma’aurata da ’yarsu yayin wani hari da suka kai a unguwar Filin Canada da ke Sabuwar Unguwa a...

Hanyoyin Da Matasa Ya Kamata Su Bi Domin Gina Rayuwarsu Tun Kafin Tsufa – Inji Ameer Salisu Yaro

Da yake ƙarin haske kan shawarwarin, ya ce ‎lokacin samartaka da ƙuruciya ba kawai mataki ne na rayuwa kaɗai ba, mataki ne wanda ake gina...

Most Popular