HomeSashen HausaBello Turji Ya Saki Mutane 32, Ya Amince Da Dakatar Da Hare-Hare...

Bello Turji Ya Saki Mutane 32, Ya Amince Da Dakatar Da Hare-Hare a Zamfara.

-

Riƙaƙƙen ɗan bindiga da aka daɗe ana nema, Bello Turji, ya saki mutane 32 da ya yi garkuwa da su, tare da amincewa da dakatar da hare-haren da ke hana manoma shiga gonaki a ƙaramar hukumar Shinkafi, ta jihar Zamfara.

Wannan na zuwa ne bayan tattaunawar sulhu da wasu malamai suka jagoranta, kamar yadda fitaccen malamin addini, Sheikh Musa Yusuf (Asadus-Sunnah), ya bayyana a wata Huɗuba da ya gabatar a Kaduna.

A cewarsa, tattaunawar ta samu ne da haɗin gwiwar al’ummar Shinkafi domin samun damar komawa gonaki cikin dajin Fakai. Taron sulhun ya gudana sau uku a watan Yuli, inda suka gana da manyan kwamandoji kamar Bello Turji, Dan Bakkolo (wanda ya ƙaryata jita-jitar mutuwarsa), Black, Kanawa da Malam Ila.

Ƴan bindigar sun miƙa wasu makamai, tare da amincewa da barin manoma su ci gaba da ayyukansu. A matsayin kyautar sulhu, Turji ya saki mutane 32 – ciki har da mata da yara, wasu daga cikinsu sun kwashe watanni a tsare, wasu kuma sun haihu a daji. Daya daga cikin su ya kamu da ciwon cizon maciji.

An kuma cimma matsaya cewa Fulani su riƙa yawo cikin yanci ba tare da fargabar farmakin sa-kai ba. Sheikh Yusuf ya ce zaman lafiya ya fara dawowa a Shinkafi sakamakon yarjejeniyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular