HomeSashen HausaMagoya Bayan APC Da Dama Sun Sauya Sheƙa Zuwa ADC a Jihar...

Magoya Bayan APC Da Dama Sun Sauya Sheƙa Zuwa ADC a Jihar Sokoto

-

A Jihar Sokoto, magoya bayan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da dama, musamman daga Ƙaramar Hukumar Gada, sun sauya sheƙa zuwa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Rahotanni daga majiyoyi mai tushe sun tabbatar da cewa waɗanda suka sauya sheƙar sun yi hakan ne saboda ƙorafin rashin tsaro, talauci, da kuma gazawar gwamnati wajen samar da ingantaccen shugabanci.

Tsohon Sanata, Abubakar Gada, wanda ya karɓi sabbin ‘yan jam’iyyar ADC, ya bayyana cewa jama’a na neman mafita daga halin da ake ciki, inda ya jaddada cewa ADC na da shirin siyasa mai ma’ana wanda zai iya kawo sauyi a rayuwar al’umma.

Inda ya ƙara da cewa:
“Mutane sun gaji da talauci da rashin aikin yi. Suna so su ga shugabanci na gaskiya da tsari mai inganci, shi ya sa suka yo dandazo zuwa ADC.”

Binciken jaridu irin su Punch Newspapers, Daily Post Nigeria, da Leadership ya nuna cewa wannan sauyin sheƙa na iya ƙara ƙarfafa ADC a Sokoto, tare da yiwuwar yin tasiri a siyasar jihar a zaben dake gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ma’aikatar Lafiya Tayi Bankwana Da Babban Sakataren Ta, Dr. Ahmed Tijjani Hamza, Bayan Wa’adin Aikinsa Ya Kare A Jihar Katsina

Ma'aikatar Lafiya ta jihar Katsina ta shirya ma Dr. Ahmed Tijjani Hamza, gagarumar liyafa, tare da karramawa, a yayin da yake bankwana da ma'aikatan sashen...

Masu Ƙwacen Waya Sun Hallaka Ma’aikaciyar Lafiya A Zariya

Wasu da ake zargin masu kwacen waya ne sun kashe ma’aikaciyar jinya a Asibitin Gambo Sawaba da ke Zariya a jihar Kaduna mai suna Hadiza...

Most Popular