A ƙoƙarin daƙile fatauci da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a Najeriya, hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Katsina haɗin guiwa da ƙungiyar Queen Dijah Women And Children Awareness Initiative, sun shirya gangamin ne domin faɗakar da al’umma kan illar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi
Lokacin da suke gudanar da gangamin wayar da kan al’umma, sun zagaya a wasu titunan cikin garin Katsina, wanda ya yi dai-dai da ranar Laraba 25 ga watan Yuni a matsayin ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don faɗakar da al’umma.
Taron ya samu mahalartar, al’umma daban-daban, da kuma jami’an hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa FRSC, da jami’an ƴan sanda, Sojoji da jami’an tsaron farin kaya na Civil Defense, da kuma wasu ƙungiyoyin fararen hula masu yaƙi da shan miyagun kwayoyi a Katsina, daga ciki har da ƙungiyar dake rajin kare haƙƙin Mata da ƙananan Yara da masu buƙata ta musamman.
Nigerian Post ta samu cewa, mutane da dama ne suka goyi bayan Hukumar tare da yaba ma su a akan ƙwazon su na wayar da kai, gangamin bikin tunawa da ranar.
A jawabin kwamandan hukumar NDLEA a jihar Katsina, Sama’ila Ɗanmalam, ya ce sun shirya taron domin faɗakar da al’umma kan illar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi domin ganin cewa an samu al’umma tagari.
Ya ce, ita al’umma idan ta yi kyau kowanne ɓangare zai yi kyau kuma za a rinƙa samun kyakkyawan tattalin arzikin ƙasa, da kuma gujewa yawaitar samun mugayen laifuffuka a ƙasa.
Ya kuma gode ma jama’a da kuma gwamnatin jihar Katsina da ta ba su gudunmawa suka shirya taron, don wayar da kan jama’a kan illar sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya, daga ciki har da jihar Katsina.