HomeSashen HausaNDLEA sun shirya gangamin wayar da kan al'umma kan ta'ammali da miyagun...

NDLEA sun shirya gangamin wayar da kan al’umma kan ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a Katsina

-

A ƙoƙarin daƙile fatauci da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi a Najeriya, hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Katsina haɗin guiwa da ƙungiyar Queen Dijah Women And Children Awareness Initiative, sun shirya gangamin ne domin faɗakar da al’umma kan illar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi

Lokacin da suke gudanar da gangamin wayar da kan al’umma, sun zagaya a wasu titunan cikin garin Katsina, wanda ya yi dai-dai da ranar Laraba 25 ga watan Yuni a matsayin ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don faɗakar da al’umma.

Taron ya samu mahalartar, al’umma daban-daban, da kuma jami’an hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa FRSC, da jami’an ƴan sanda, Sojoji da jami’an tsaron farin kaya na Civil Defense, da kuma wasu ƙungiyoyin fararen hula masu yaƙi da shan miyagun kwayoyi a Katsina, daga ciki har da ƙungiyar dake rajin kare haƙƙin Mata da ƙananan Yara da masu buƙata ta musamman.

Nigerian Post ta samu cewa, mutane da dama ne suka goyi bayan Hukumar tare da yaba ma su a akan ƙwazon su na wayar da kai, gangamin bikin tunawa da ranar.

A jawabin kwamandan hukumar NDLEA a jihar Katsina, Sama’ila Ɗanmalam, ya ce sun shirya taron domin faɗakar da al’umma kan illar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi domin ganin cewa an samu al’umma tagari.

Ya ce, ita al’umma idan ta yi kyau kowanne ɓangare zai yi kyau kuma za a rinƙa samun kyakkyawan tattalin arzikin ƙasa, da kuma gujewa yawaitar samun mugayen laifuffuka a ƙasa.

Ya kuma gode ma jama’a da kuma gwamnatin jihar Katsina da ta ba su gudunmawa suka shirya taron, don wayar da kan jama’a kan illar sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya, daga ciki har da jihar Katsina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

PDP da APC Sun Fusata Kan Hukuncin Kotun Kanada Na Dangantasu Da Ta’addanci

Wata kotun tarayya a ƙasar Kanada ta haifar da cece-kuce bayan da ta danganta manyan jam’iyyun siyasa na Najeriya, Peoples Democratic Party (PDP) da All...

Nigeria’s Inflation Rate Eases to 21.88% in July — NBS

Nigeria’s annual inflation rate eased to 21.88% in July 2025, down from 22.22% recorded in June, according to the latest figures released by the National...

Most Popular