HomeSashen HausaTinubu ya tura Shettima a ɓoye don ya ziyarci Buhari a Asibitin...

Tinubu ya tura Shettima a ɓoye don ya ziyarci Buhari a Asibitin London

-

Shugaba Bola Tinubu ya tura mataimakinsa, Kashim Shettima, domin ya ziyarci tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a wani asibiti da ke London a ranar Litinin, kamar yadda wasu majiyoyi masu tushe su ka shaida wa jaridar TheCable.

Tsohon shugaban ya dade yana fama da rashin lafiya, kamar yadda Empowered Newswire ta fara rawaito wa, amma ana ganin yana samun sauƙi a halin yanzu.

Shettima ya kasance a Addis Ababa, Habasha, a gayyatar Firayim Minista Abiy Ahmed Ali domin halartar ƙaddamar da shirin Green Legacy Initiative (GLI) na ƙasar ta Gabashin Afirka.

Stanley Nkwocha, mai magana da yawun Shettima, shi ne ya tabbatar da cewa, shugabansa ya kai ziyara London amma ya ce ba zai iya cewa komai game da manufar ziyarar ba domin bai san cikakken jadawalin tafiyar ba.

Sai dai Tinubu wanda ke wata ziyara ta ƙasa a St Lucia, ya umurci Shettima da ya tafi London domin duba tsohon shugaban ƙasar.

TheCable ta fahimci cewa, Shugaba Tinubu ya umarci Shettima da ya binciki yanayin lafiyar Buhari tare da tabbatar da an ba shi kulawa ta musamman har zuwa samun lafiya.

Shettima wanda ya tashi daga Addis Ababa a daren Lahadi, inda ya isa London ranar Litinin kafin ya tafi wani Asibiti da ba a bayyana sunansa ba domin isar da saƙon Tinubu ga Buhari, in ji majiyoyin.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Gwamnan Katsina Ya Zama Abin Koyi Ga Sauran Jihohin Najeriya— Inji Kashim Shettima

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya zama abin koyi idan akai duba da...

Budurwa Ta Hallaka Kanta A Jihar Borno Bayan Tilasta Ma Ta Auren Dole

Wata matashiya ta kashe kanta a karamar hukumar Gubio ta jihar Borno, bayan mahaifinta ya tilasta mata aure da ɗaya daga cikin abokansa.   Shafin jaridar Zagazola...

Most Popular