HomeSashen HausaAn Maido Mabarata 13 Yan Asalin Jihar Katsina Daga Birnin Tarayya Abuja

An Maido Mabarata 13 Yan Asalin Jihar Katsina Daga Birnin Tarayya Abuja

-

Gwamnatin Jihar Katsina ta karɓi wasu mutane su 13 yan asalin jihar, da aka maido daga Birnin Tarayya Abuja da suke yawon Bará

Kwamishinan Raya Karkara Da Walwalar Jama’a Farfesa Abdulhamid Ahmed, shi ne ya karbi mutanen a madadin Gwamnatin Jiha.

A rahoton da Nigerian Post ta samu, Mataimakin Darakta a Sashen Walwala da Jin Dadin Jama’a na Birnin Tarayya ne ya miƙa mutanen ga Kwamishina, a lokacin wani taro da ya gudana a Ma’aikatar Raya Karkara ta jihar Katsina.

Da yake miƙa mutanen, Mataimakin Daraktan ya yabawa Gwamnatin Jihar Katsina a kan kyakkyawar tarba da Gwamnatin Jihar Katsina ta yi wa tawwagar su.

Ya ce an maido mutanen ne a ƙarƙashin shirin tsabtace Birnin Tarayya Abuja daga bárace-bárace da masu bola jari gami da masu kwana a kangaye.

Mataimakin Daraktan ya ce Ministan Abuja ne ya ƙirƙiro shirin, daga nan sai ya buƙaci waɗanda aka maido a kan su nesanta kan su daga halinda suka fita.

A nashi jawabin, Kwamishinan Ma’aikatar Raya Karkara Da Walwalar Jama’a Farfesa Abdulhamid Ahmed, ya yaba wa Sashen Walwalar Jama’a na Birnin Tarayya akan maido da mutanen cikin koshin lafiya.

Farfesa Abdulhamid Ahmed ya tabbatar da cewa ma’aikatar zata kula da mutanen kafin a mika su ga iyalan su nan ba da jimawa ba.

Daga karshe ya bukace su akan su kasance masu halayya ta gari bayan an maida su ga iyalan su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular