HomeSashen HausaKatsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

Katsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

-

Katsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

Katsina United ta samu nasarar doke abokiyar hamayyarta, Kano Pillars, da ci 1–0 a wasan gasar Firimiya lig na Kwararru ta Najeriya da aka fafata a filin wasa na Muhammadu Dikko, cikin garin Katsina.

An buga wasan ne cikin tsananin ƙwarewa da hazaƙa inda bangarorin biyu suka nuna gogwarsu su a fagen kwallon kafa, sai dai mintuna na ƙarshen wasa ne Katsina United ta samu damar zura kwallo ta hannun ɗan wasanta, Azeez Falalu, wanda hakan ya bai wa masu masaukin baƙi nasara.

Magoya baya daga sassa daban-daban na jihar Katsina da Kano ne dai, suka halarci wasan, inda suka nuna farin cikinsu ko da yake sakamakon bai yi ma wasu dadi ba.

Hukumar gudanar da wasa ta tabbatar da cewa wannan nasara ta Katsina United zai ƙara mata maki a teburin gasar, yayin da Kano Pillars za ta sake ƙoƙari a wasanta na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina State Government To Reward Athletes Who Attaracts Medals To The State

The commissioner of sports and youth development Alh Aliyu Lawal Zakari Shargalle has reaffirm the state government commitment to reward any athlete who attracts medals...

NSCDC Ta Cika Hannunta Da Sojin Bogi A Jihar Katsina

Hukumar Tsaro Ta Farin Kaya Ta (NSCDC) Reshen Jihar Katsina Ta Kama wanda ake zargi da sojan gona amatsayin ma'aikacin hukumar a yan'kin unguwar kwado...

Most Popular