HomeSashen HausaKatsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

Katsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

-

Katsina United Ta Doke Kano Pillars Da 1-0 A Muhammadu Dikko Stadium

Katsina United ta samu nasarar doke abokiyar hamayyarta, Kano Pillars, da ci 1–0 a wasan gasar Firimiya lig na Kwararru ta Najeriya da aka fafata a filin wasa na Muhammadu Dikko, cikin garin Katsina.

An buga wasan ne cikin tsananin ƙwarewa da hazaƙa inda bangarorin biyu suka nuna gogwarsu su a fagen kwallon kafa, sai dai mintuna na ƙarshen wasa ne Katsina United ta samu damar zura kwallo ta hannun ɗan wasanta, Azeez Falalu, wanda hakan ya bai wa masu masaukin baƙi nasara.

Magoya baya daga sassa daban-daban na jihar Katsina da Kano ne dai, suka halarci wasan, inda suka nuna farin cikinsu ko da yake sakamakon bai yi ma wasu dadi ba.

Hukumar gudanar da wasa ta tabbatar da cewa wannan nasara ta Katsina United zai ƙara mata maki a teburin gasar, yayin da Kano Pillars za ta sake ƙoƙari a wasanta na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular