HomeSashen HausaGwamna Abba Ya Aika Sunayen Kwamishinoni Biyu Zuwa Majalisar Dokokin Kano

Gwamna Abba Ya Aika Sunayen Kwamishinoni Biyu Zuwa Majalisar Dokokin Kano

-

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya aika sunayen mutane biyu zuwa Majalisar Dokokin Kano domin tantancewa a matsayin sabbin Kwamishinoni kuma mambobin majalisar zartarwa ta jiha.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar, gwamnan ya gabatar da sunayen Barrister Abdulkarim Kabir Maude daga Minjibir, wanda zai karÉ“i matsayin Babban Lauya na S (SAN) a gaban kotun koli gobe, da kuma Dr. Aliyu Isa Aliyu, Farfesa a fannin lissafi daga jami’ar North West U, Kano.

Barr. Maude, mai shekara 40, ya yi fice a harkar shari’a inda ya yi aiki fiye da shekara goma, kuma yana da digiri daga jami’o’i daban-daban ciki har da Jami’ar ABU Zaria da BUK.

Shi kuwa Dr. Aliyu, mai shekara 41, ya kware a fannin lissafi inda ya yi karantu a Najeriya da Jordan da Turkiyya, kuma yanzu haka shi ne Darakta Janar na Hukumar Ƙididdiga ta Jihar Kano.

A wani ɓangare, Gwamna Yusuf ya kuma amince da nadin Barrister Salisu Muhammad Tahir a matsayin sabon Babban Lauyan jiha (Solicitor-General) da Babban Sakataren na Ma’aikatar Shari’a ta Jiha.

Gwamnan ya ce shigar da sabbin mambobin majalisar zartarwa na daga cikin matakan da gwamnatinsa ke É—auka domin tabbatar da cancanta da kwarewa da gaskiya a aikin gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Hukumar NSCDC A Katsina Ta Yi Sabon Shugaba

Hukumar Tsaro ta NSCDC reshen Jihar Katsina ta samu sabon kwamanda bayan sauyin shugabanci da ya gudana a ranar Litinin, 22 ga watan Satumba, 2025.   A...

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Horas Da Malamai 250 Da Faransifal 50, Don Inganta Ilmin Jihar

Ma’aikatar Ilimi a Matakin Farko da na Sakandire a jihar Katsina, haɗin gwiwa da Majalisar Turai (British Council), ta ƙaddamar da wani muhimmin shirin horaswa...

Most Popular