Ƙasar Indonesia Ta Dakatar Da Lasisin Manhajar Tiktok Saboda Ƙin Bada Bayanai
Gwamnatin Indonesia ta dakatar da lasisin gudanarwar manhajar Tiktok a ƙasar, bayan kamfanin ya ƙi bayar da bayanan ga Gwamnati wanda ta nema dangane da zanga-zangar nuna adawa da gwamnati waddda aka gudanar a baya-bayan nan.
Ma’aikatar Sadarwa da Harkokin Dijital ta Indonesia ta bayyana hakan a ranar Juma’ar cewa wannan mataki ya zama dole ne saboda ƙin bin ƙa’idar da ke wajabta wa kamfanonin sadarwa bayar da bayanai idan hukumomi suka buƙata.
Indonesia na daga cikin manyan ƙasashe masu amfani da TikTok a duniya, musamman tsakanin matasa. Wannan mataki zai iya shafar harkokin sadarwa da kasuwancin yanar gizo a kasar, inda daruruwan dubban ‘yan kasuwa ke amfani da TikTok wajen tallata kayayyaki da kuma mu’amala.
Kafar Reuters ta Bayyana cewa hukumomin sun tabbatar da dakatarwar za ta ci gaba da wakana har sai an cimma matsaya tsakanin gwamnati da kamfanin TikTok, kan yadda za a gudanar da musayar bayanai da kuma bin ƙa’idojin tsaro na ƙasar.