HomeSashen HausaNSCDC, Rundunar ‘Yan'sanda Da DSS, Sun Jaddada Cigaba da Hadin Gwaiwa Don...

NSCDC, Rundunar ‘Yan’sanda Da DSS, Sun Jaddada Cigaba da Hadin Gwaiwa Don Yaƙi Da Aikata Laifuka A Jihar Katsina

-

NSCDC, Rundunar ‘Yan’sanda Da DSS, Sun Jaddada Cigaba da Hadin Gwaiwa Don Yaƙi Da Aikata Laifuka A Jihar Katsina

Hukumar Tsaro ta Civil Defence (NSCDC) reshen jihar Katsina da takwarorinta na Rundunar ‘Yansanda (NPF) da Hukumar Tsaro ta DSS sun sake jaddada ƙudurorinsu na yin aiki tare domin kawar da laifuka da aikata miyagun ayyuka a fadin Jihar.

Nigerian Post ta bibiyi cewa, yunkurin jaddada ya biyo bayan wata ziyarar ban girma da Kwamandan Jihar, AD Moriki Acti, Anim ya kai wa Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Bello Shehu, da Daraktan DSS na Jihar, Musa Muhammad Yankari, a hedikwatocinsu da ke Katsina.

A jawabinsa, Kwamanda Moriki ya bayyana cewa ziyarar ta zo ne domin ƙarfafa dangantakar da ke tsakanin NSCDC da sauran hukumomin tsaro, tare da neman ci gaba da haɗin kai da fahimtar juna.

“Ziyarar yau ba wai neman haɗin kai muka zo ba, amma domin ƙarfafa dangantakar da tuni ta riga ta kasance tsakanin NSCDC da hukumarku,” in ji Kwamanda Moriki.

Ya kuma bayyana godiya bisa tarbar da suka samu daga hukumomin biyu, tare da taimakon da suke baiwa hukumar a cikin Jihar. Ya jaddada cewa kokarin yaƙi da laifi a Jihar Katsina zai fi samun nasara idan kowa ya haɗa hannu wajen tabbatar da tsaron jama’a, kare rayuka, da kuma kiyaye muhimman kadarori da ababen more rayuwa na gwamnati.

A martaninsu daban-daban, Kwamishinan ‘Yan Sanda da Daraktan DSS sun tarbi sabon Kwamanda zuwa Katsina tare da nuna farin ciki da ziyarar tasa. Sun kuma sake jaddada aniyarsu ta ci gaba da gina kyakkyawar dangantaka ta aiki tare da NSCDC a cikin Jihar.

Bayanin hakan na ƙunshe acikin wata sanarwa da Jami’in hulda da Jama’a na hukumar SC Buhari Hamisu ya fitar a katsina.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular