HomeSashen HausaƊan Wasan Ƙwallon Ƙafa Na Togo, Samuel Asamoah, Ya Karya Wuya A...

Ɗan Wasan Ƙwallon Ƙafa Na Togo, Samuel Asamoah, Ya Karya Wuya A Wani Wasa A Ƙasar China

-

Dan wasan tsakiyar ƙasar Togo, Samuel Asamoah, ya karye a wuya bayan karo da allon talla na gefen fili yayin wasa a kasar Sin, lamarin da kungiyar ƙwallon ƙafar da ya ke taka leda ta ce da wuya idan bai samu ciwon laka ba.

 

Asamoah, mai shekaru 31, wanda ke buga kwallo a kungiyar ƙwallon ƙafa ta Guangxi Pingguo na rukuni na biyu a kasar, ya bugu da kai cikin allon talla na LED bayan wani dan wasan abokan hamayya ya tura shi yayin wasan cikin gida da aka buga a ranar Lahadi.

 

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, kulob din Guangxi Pingguo ya bayyana cewa dan wasan yana cikin hadarin samun nakasar kafa (high-level paraplegia) bayan an gano yana da karaya da dama a wuya tare da raunin jijiyoyi masu tsanani.

 

An bayyana cewa an yi wa Asamoah tiyata kuma yana cikin halin da ya daidaita, yayin da kulob din ya ce za a ci gaba da sanar da jama’a ci gaban murmurewarsa bayan ƙarin gwaje-gwaje.

 

A yayin wasan, dan wasan tsakiyar Chongqing Tonglianglong, Zhang Zhixiong, ya karɓi katin gargadi saboda tura Asamoah cikin allon talla.

 

Asamoah ya shafe yawancin aikinsa a ƙasar Belgium kafin ya koma China a shekarar 2024, kuma yana da wasanni shida da ya wakilci ƙasar Togo a matakin kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Budurwa Ta Hallaka Kanta A Jihar Borno Bayan Tilasta Ma Ta Auren Dole

Wata matashiya ta kashe kanta a karamar hukumar Gubio ta jihar Borno, bayan mahaifinta ya tilasta mata aure da ɗaya daga cikin abokansa.   Shafin jaridar Zagazola...

An Fara Binciken Tsohon Gwamna Daga Kudanci Kan Zargin Kitsa Juyin Mulki A Najeriya

Rahotanni sun bayyana cewa ana binciken wani tsohon gwamna daga ɗaya daga cikin jihohin kudancin Najeriya bisa zargin alaƙa da wasu jami’an soji 16 da...

Most Popular