HomeSashen HausaGwamnatin Taraiya Ta Bada Umarnin A Riƙa Rera Baitin Farko Kaɗai Na...

Gwamnatin Taraiya Ta Bada Umarnin A Riƙa Rera Baitin Farko Kaɗai Na Taken Nijeriya A Wajen Taruka

-

Hukumar Wayar da kan Ƴan ƙasa (NOA) ta fitar da sabbin ka’idoji game da yadda za a rera taken ƙasar Najeriya.

 

An fitar da wannan umarni mai ɗauke da bayanai huɗu ne a cikin wata sanarwa da aka saki a ranar Alhamis.

 

Sanarwar ta ce: “A rera ko a karanta baitin farko kawai (ba duka baitoci uku ba) a dukkan tarukan gwamnati.”

 

“Haka kuma baitin na uku shi ne za a karanta a matsayin Addu’ar Ƙasa a farkon kowane taro.”

 

“Dukkan baitoci uku na taken ƙasa za a rera su ne kawai a lokutan musamman kamar Ranar ‘Yancin Kai da Ranar Rantsar Shugaban Ƙasa da Ranar Tunawa da Sojoji da Ranar Dimokuraɗiyya (12 ga Yuni), da Ranar Rantsar da Majalisar Dokoki ta Ƙasa, da sauransu.”

 

A watan Mayun da ya gabata, Shugaba Bola Tinubu ya sanya hannu kan kudirin da ya dawo da tsohon taken ƙasa mai taken ‘Nigeria, We Hail Thee’.

 

Wannan taken ya maye gurbin tsohon da aka rika rerawa tun daga shekarar 1978 mai taken ‘Arise, O Compatriots’.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Masu Ƙwacen Waya Sun Hallaka Ma’aikaciyar Lafiya A Zariya

Wasu da ake zargin masu kwacen waya ne sun kashe ma’aikaciyar jinya a Asibitin Gambo Sawaba da ke Zariya a jihar Kaduna mai suna Hadiza...

Gwamnan Katsina Ya Zama Abin Koyi Ga Sauran Jihohin Najeriya— Inji Kashim Shettima

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Raɗɗa, ya zama abin koyi idan akai duba da...

Most Popular