HomeSashen HausaGwamnatin Taraiya Ta Bada Umarnin A Riƙa Rera Baitin Farko Kaɗai Na...

Gwamnatin Taraiya Ta Bada Umarnin A Riƙa Rera Baitin Farko Kaɗai Na Taken Nijeriya A Wajen Taruka

-

Hukumar Wayar da kan Ƴan ƙasa (NOA) ta fitar da sabbin ka’idoji game da yadda za a rera taken ƙasar Najeriya.

 

An fitar da wannan umarni mai ɗauke da bayanai huɗu ne a cikin wata sanarwa da aka saki a ranar Alhamis.

 

Sanarwar ta ce: “A rera ko a karanta baitin farko kawai (ba duka baitoci uku ba) a dukkan tarukan gwamnati.”

 

“Haka kuma baitin na uku shi ne za a karanta a matsayin Addu’ar Ƙasa a farkon kowane taro.”

 

“Dukkan baitoci uku na taken ƙasa za a rera su ne kawai a lokutan musamman kamar Ranar ‘Yancin Kai da Ranar Rantsar Shugaban Ƙasa da Ranar Tunawa da Sojoji da Ranar Dimokuraɗiyya (12 ga Yuni), da Ranar Rantsar da Majalisar Dokoki ta Ƙasa, da sauransu.”

 

A watan Mayun da ya gabata, Shugaba Bola Tinubu ya sanya hannu kan kudirin da ya dawo da tsohon taken ƙasa mai taken ‘Nigeria, We Hail Thee’.

 

Wannan taken ya maye gurbin tsohon da aka rika rerawa tun daga shekarar 1978 mai taken ‘Arise, O Compatriots’.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular