HomeSashen HausaGwamnatin Taraiya Ta Bada Umarnin A Riƙa Rera Baitin Farko Kaɗai Na...

Gwamnatin Taraiya Ta Bada Umarnin A Riƙa Rera Baitin Farko Kaɗai Na Taken Nijeriya A Wajen Taruka

-

Hukumar Wayar da kan Ƴan ƙasa (NOA) ta fitar da sabbin ka’idoji game da yadda za a rera taken ƙasar Najeriya.

 

An fitar da wannan umarni mai ɗauke da bayanai huɗu ne a cikin wata sanarwa da aka saki a ranar Alhamis.

 

Sanarwar ta ce: “A rera ko a karanta baitin farko kawai (ba duka baitoci uku ba) a dukkan tarukan gwamnati.”

 

“Haka kuma baitin na uku shi ne za a karanta a matsayin Addu’ar Ƙasa a farkon kowane taro.”

 

“Dukkan baitoci uku na taken ƙasa za a rera su ne kawai a lokutan musamman kamar Ranar ‘Yancin Kai da Ranar Rantsar Shugaban Ƙasa da Ranar Tunawa da Sojoji da Ranar Dimokuraɗiyya (12 ga Yuni), da Ranar Rantsar da Majalisar Dokoki ta Ƙasa, da sauransu.”

 

A watan Mayun da ya gabata, Shugaba Bola Tinubu ya sanya hannu kan kudirin da ya dawo da tsohon taken ƙasa mai taken ‘Nigeria, We Hail Thee’.

 

Wannan taken ya maye gurbin tsohon da aka rika rerawa tun daga shekarar 1978 mai taken ‘Arise, O Compatriots’.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Tsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu A Najeriya

A wani rahoto da Nigerian Post ta samu daga Aminiya, an tabbatar da cewa, tsofaffin ma’aikatan (FRCN) Federal Radio Corporation of Nigeria (FRCN) sun ce...

Mace Mai Juna Biyu Ta Rasa Ranta Bayan Ma’aikaci Ya Ki Karɓar Transfer Don Biyan Kudin Iskar Numfashi A Asibitin Turai Katsina

Mace Mai Juna Biyu Ta Rasa Ranta Bayan Ma’aikaci Ya Ki Karɓar Transfer Don Biyan Kudin Iskar Numfashi A Asibitin Turai Katsina Wata mata mai juna...

Most Popular