HomeSashen HausaAn ci tarar Katsina United Miliyan 9 da hana su buga wasa...

An ci tarar Katsina United Miliyan 9 da hana su buga wasa a Gida

-

Hukumar NPFL mai kula da gasar ƙwallon ƙafa ta firimiyar Najeriya ta ci tarar ƙungiyar Katsina United naira miliyan tara sakamakon hatsaniyar da magoya bayanta suka tayar ranar Asabar.

Wata sanarwa da NPFl ta fitar a yau ta ce mahukuntan Katsina United sun gaza “samar da cikakken tsaro abin da ya jawo magoya baya suka shiga cikin fili” a wasansu da Barau FC a garin na Katsina.

Magoya bayan Katsina sun auka cikin filin ne jim kaɗan bayan Barau ta farke ƙwallon da Katsina ta zira mata, inda ɗaya daga cikinsu ya ji wa ɗanwasan barau rauni a wuya.

“An ci tarar kulob ɗin naira miliyan ɗaya kan kowane laifi uku da suka haɗa da jejjefa abubuwa cikin fili, da rashin tsawatar wa magoya, da kuma haddasa hatsaniya yayin wasa,” in ji sanarwar.

“Haka kuma, Katsina za ta biya tarar miliyan biyu kan gazawa wajen samar da cikakken tsaro a filin wasa.

“Sannan za ta biya miliyan biyu kan kowane laifi biyu na ɗaukar nauyin gyaran motocin Barau FC da aka lalata, da kuma ɓata wa alƙalan wasa da ‘yan Barau FC lokaci bayan tashi daga wasan.”

Jimilla Katsina United za ta biya tarar naira miliyan tara kenan, amma NPFL ta ce tana da 48 na ɗaukaka ƙarar hukuncin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano

Ɓarawo Ya Sace Motar Ayarin Mataimakin Gwamna A Gidan Gwamnatin Kano Wani barawon mota ya kutsa cikin Gidan Gwamnatin Kano da sanyin safiyar Litinin ya kuma...

‎Yansanda Sun Kama Masu Aikata Laifuka Daban-daban, Sun Ceto Mutane 47 da Aka Yi Garkuwa da Su a Jihar Katsina

Rundunar ‘Yansanda ta Jihar Katsina ta bayyana cewa ta samu nasarori masu yawa a yakin da take yaki da laifuka, ciki har da kama mutanen...

Most Popular