HomeSashen HausaZa mu ƙarar da 'Yanbindiga a shekara ɗaya idan har Gwamnati za...

Za mu ƙarar da ‘Yanbindiga a shekara ɗaya idan har Gwamnati za ta goya mana baya– inji CJTF

-

Haɗakar Jami’an Tsaron Sa-kai na Ƙasa (CJTF) ta ci alwashin karar da ƴanbindiga da ke addabar wasu sassa na Arewacin Nijeriya a cikin shekara ɗaya take.

 

Farfesa Kailani Muhammad, Shugaban CJTF na Ƙasa ne ya baiyana hakan yayin da Charles Omini, Jakadan Musamman na Kungiyar Kare Hakkin Dan’adam na Afrika ta Yamma ya mika masa takardar zama ɗan hadaddiyar kungiyar jami’an sa-kai ta Afirka ta Yamma (JTF) a Abuja a ranar Asabar.

 

A cewar Muhammad, da Gwamnatin Tarayya ta ba da ƙarfi tare da tallafa wa CJTF kayan aiki,’ da suka dace to za su murƙushe ’yan bindiga cikin shekara guda.

 

Ya yi kira ga gwamnati da ta ba Civilian JTF goyon bayan da ya dace domin su nuna abin da za su iya yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎DA ƊUMI-ƊUMI: ’Yan Bindiga Sun Sace Dalibai 25 a Kebbi, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta

‎Fargaba da tashin hankali sun mamaye al’ummar Maga, cikin ƙaramar hukumar Danko/Wasagu ta jihar Kebbi, bayan wasu ’yan bindiga sun afka Government Girls Comprehensive Senior...

DA ƊUMI-ƊUMI: Soja AM Yerima Ya Tsallake Rijiya Da Baya Yau A Abuja

Wani matashin jami’in Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, Lt. A.M. Yarima, wanda ya yi rashin jituwa kwanan nan da Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike,...

Most Popular