HomeSashen HausaRundunar Sojin Sama Ta Yi Luguden Wuta Kan Maɓoyar Yanta'adda A Dajin...

Rundunar Sojin Sama Ta Yi Luguden Wuta Kan Maɓoyar Yanta’adda A Dajin Sambisa

-

Rundunar Sojin Sama ta Ƙasa ta ce ta ƙaddamar da luguden wuta mai ƙarfi a Arra, wani sanannen mafakar ƴan ta’adda a Sambisa.

 

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Hulɗa da Jama’a da Bayar da Bayanai, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar a jiya Laraba a Abuja.

 

Ya ce an gudanar da luguden ne bayan umarnin da Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Sunday Aneke, ya bayar.

 

Ejodame ya ce an kai harin ne bayan bayanan sirri da sa ido da kuma bincike da suka gano motsin ‘yan ta’adda bayan kwanton ɓaunar da aka yi a Kashomri ranar 17 ga Oktoba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

An Zaɓi Hon. Dauda Kurfi A Matsayin Shugaban Ƙungiyar Tsofaffin Kansiloli A Jihar Katsina

Tsofaffin Kansiloli, sun rushe shugabancin ƙungiyar tsofaffin Kansilolin ta ƙasa reshen jihar Katsina, inda suka zaɓi Hon. Dauda Kurfi, a matsayin shugaban ƙungiyar tsofaffin Kansiloli...

Dikko Radda Ya Amince Da Naɗin Sabbin Manyan Sakatarori a Jihar Katsina

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya amince da naɗin sabbin manyan sakatarorin jihar.   Gwamnan ya ce an gudanar da naɗin bi sa cancanta da...

Most Popular