HomeSashen HausaRundunar Sojin Najeriya Sun Kama Wani Fitaccen Mai Garkuwa Da Mutane A...

Rundunar Sojin Najeriya Sun Kama Wani Fitaccen Mai Garkuwa Da Mutane A Taraba

-

Rundunar ta kama mai suna Alhaji Abubakar Bawa a Kudancin Taraba.

 

Ana zargin Bawa yana da alaƙa da wani shahararren mai garkuwa da mutane, Umar Musa, wanda aka kama a kwanakin baya.

 

Binciken ya nuna suna cikin wata babbar ƙungiyar laifuka da ke da alhakin garkuwa da mutane da kai hare-hare a yankin.

 

Kwamandan Brigade ta 6 ya yaba wa sojoji bisa nasarar, yana mai cewa Operation Zafin Wuta na yunƙuri wajen lalata ƙungiyoyin dake aikata laifuka, kuma za su ci gaba da aiki ba tare da sassauci ba.

 

Sojoji suna cigaba da bincike kan sauran abokan hulɗar wanda aka kama, kuma Rundunar Soji tayi kira ga jama’a da su riƙa bayar da bayanai. Bawa yana tsare yanzu kuma ana ci gaba da tambayarsa.

 

Daga Aliyu Adamu Tsiga

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular