HomeSashen HausaRundunar Sojin Najeriya Sun Kama Wani Fitaccen Mai Garkuwa Da Mutane A...

Rundunar Sojin Najeriya Sun Kama Wani Fitaccen Mai Garkuwa Da Mutane A Taraba

-

Rundunar ta kama mai suna Alhaji Abubakar Bawa a Kudancin Taraba.

 

Ana zargin Bawa yana da alaƙa da wani shahararren mai garkuwa da mutane, Umar Musa, wanda aka kama a kwanakin baya.

 

Binciken ya nuna suna cikin wata babbar ƙungiyar laifuka da ke da alhakin garkuwa da mutane da kai hare-hare a yankin.

 

Kwamandan Brigade ta 6 ya yaba wa sojoji bisa nasarar, yana mai cewa Operation Zafin Wuta na yunƙuri wajen lalata ƙungiyoyin dake aikata laifuka, kuma za su ci gaba da aiki ba tare da sassauci ba.

 

Sojoji suna cigaba da bincike kan sauran abokan hulɗar wanda aka kama, kuma Rundunar Soji tayi kira ga jama’a da su riƙa bayar da bayanai. Bawa yana tsare yanzu kuma ana ci gaba da tambayarsa.

 

Daga Aliyu Adamu Tsiga

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Nijeriya Ta Musanta Zargin Leken Asiri Kan Jirginta Da Ke Burkina-Faso

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da ke cewa jirginta kirar C-130 da ya sauka ba tare da shiri ba a Bobo-Dioulasso,...

Duniya Za Ta Fuskanci Ƙalubale, Idan Najeriya Ta Wargaje– Inji Sanata Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa a Najeriya, Kashim Shettima ya ce gwamnatin Tinubu ba za ta taɓa bari Najeriya ta ruguje a hannunta ba, komai rintsi.   Kamar yadda...

Most Popular