HomeSashen HausaTsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu...

Tsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu A Najeriya

-

A wani rahoto da Nigerian Post ta samu daga Aminiya, an tabbatar da cewa, tsofaffin ma’aikatan (FRCN) Federal Radio Corporation of Nigeria (FRCN) sun ce sun shirya gudanar zanga-zanga tsirara a gobe Litinin 8 ga Disamba na shekarar 2025.

 

Shugaban ƙungiyar, Mista Mukaila Ogunbote, shi ne ya tabbatar da hakan, inda ya ce za su shiga zanga-zangar ne domin maƙalewar wasu haƙƙoƙinsu da gwamnati ta gaza biya kamar yadda sakataren kuɗi na ƙungiyar tsofaffin ma’aikatan, Bola Popoola ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar a Legas.

 

Sun jaddada cewa, lamarin ya kai su bango ne shiyasa suke ƙoƙarin gudanar da zanga-zangar ko Gwamnatin tarayya za ta waiwayo a garesu.

 

Wannan dai, ba shi ne karon farko da ‘yan ƙasa gamida masu aiki a ƙasar ke yawan yin barazana na yin zanga-zanga a Najeriya, wanda ko a makonnin da suka gaba ASSUU ta yi Barazanar tsunduma yajin aiki jim kadan bayan da suka gama jan kunne ga wata zanga-zangar lumana a yankunan ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Mace Mai Juna Biyu Ta Rasa Ranta Bayan Ma’aikaci Ya Ki Karɓar Transfer Don Biyan Kudin Iskar Numfashi A Asibitin Turai Katsina

Mace Mai Juna Biyu Ta Rasa Ranta Bayan Ma’aikaci Ya Ki Karɓar Transfer Don Biyan Kudin Iskar Numfashi A Asibitin Turai Katsina Wata mata mai juna...

Hadiza Gabon Na Shirin Barin Kaduna Zuwa Kano Da Shirin Talk Show

Daya daga cikin makusantar tsohuwar Jarumar Kanywood Hadiza Gabon, ya tabbatar wa Jaridar ALFIJIR NEWS, wanda a yanzu jarumar ta fara tinanin dauke zauren Shirin...

Most Popular