HomeSashen HausaTsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu...

Tsofaffin Ma’aikatan FRCN, Sun Shirya Jagorantar Zanga-zanga Zígídír, Kan Ƙin Biyansu Haƙƙinsu A Najeriya

-

A wani rahoto da Nigerian Post ta samu daga Aminiya, an tabbatar da cewa, tsofaffin ma’aikatan (FRCN) Federal Radio Corporation of Nigeria (FRCN) sun ce sun shirya gudanar zanga-zanga tsirara a gobe Litinin 8 ga Disamba na shekarar 2025.

 

Shugaban ƙungiyar, Mista Mukaila Ogunbote, shi ne ya tabbatar da hakan, inda ya ce za su shiga zanga-zangar ne domin maƙalewar wasu haƙƙoƙinsu da gwamnati ta gaza biya kamar yadda sakataren kuɗi na ƙungiyar tsofaffin ma’aikatan, Bola Popoola ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar a Legas.

 

Sun jaddada cewa, lamarin ya kai su bango ne shiyasa suke ƙoƙarin gudanar da zanga-zangar ko Gwamnatin tarayya za ta waiwayo a garesu.

 

Wannan dai, ba shi ne karon farko da ‘yan ƙasa gamida masu aiki a ƙasar ke yawan yin barazana na yin zanga-zanga a Najeriya, wanda ko a makonnin da suka gaba ASSUU ta yi Barazanar tsunduma yajin aiki jim kadan bayan da suka gama jan kunne ga wata zanga-zangar lumana a yankunan ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎An Cafke Wani Mutum Da Zargin Sayar Da Jaririn ‘Yar’ uwarsa Naira Miliyan 2 a Legas

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta kama wani mutum mai shekaru 30 da haihuwa bisa zargin sayar da jaririn ‘yar uwarsa mai wata daya kacal...

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi

An Damƙa Walida Ga Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Namadi Ɗanmoɗi Hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun damƙa matashiya Walida Abdullahi Ibrahim ga Gwamnan Jihar Jigawa,...

Most Popular