HomeSashen HausaAmurka Ta Ƙwace Wani Babban Jirgin Dakwan Mai Na Najeriya

Amurka Ta Ƙwace Wani Babban Jirgin Dakwan Mai Na Najeriya

-

Dakarun tsaron gabar tekun Amurka da ke aiki tare da sojojin ruwan ƙasar, sun kama wani babban jirgin ruwa na Najeriya da ake kira da Skipper, sakamakon yadda ake zargin ana amfani da jirgin wajen satar danyen mai da fashin teku da dai sauran laifukan da suka shafi ƙasa da ƙasa.

 

A cewar jami’an tsaron Amurka, sun kama jirgin ruwan ne a lokacin da suke aiwatar da wani aikin a ƙarƙashin dokar tabbatar da doka da oda ta ƙasar, wacce shugaba Donald Trump ya sanar.

 

Hukumomin sun bayyana cewa, a lokacin da aka kama jirgin ruwan na dakon mai, akwai tutar ƙasar Guyana a jikinsa.

 

Nigerian Post ta bibiyi cewa, sai dai sashen da ke kula da harkokin jiragen ruwan ƙasar ta Guyana, ya ce ko kaɗan jirgin baya da rijista da su, kuma yana amfani da tutar ƙasar ne ta haramtatciyar hanya.

 

Ita ma dai hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ruwa ta Najeriya ta bakin mai magana da yawunta Edward Osagie, ya ce basu da masani kan lamarin a hukumance.

 

Bayaga hukumar NIMASA, shima shugaban ƙungiyar masu jiragen ruwa ta Najeriya Otunba Sola Adewuni, ya ce baya da wasu gamsassun bayanai kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Governor Dikko Radda Inaugurates Katsina State Council of Emir’s

Katsina State Governor has inaugurated the State Council of Emirs with the Emir of Katsina Alhaji Abdulmumini Kabir as the Chairman while his Daura counterpart...

SUBEB Chairman Reiterates Need for Compliance with Minimum Standards for School Infrastructure in Katsina

Executive Chairman Katsina State Universal Board has restated necessity of complying Minimum Standard for Schools' Infrastructure in the state.   Dr. Kabir Magaji Gafiya stated this during...

Most Popular