HomeSashen HausaAmurka Ta Ƙwace Wani Babban Jirgin Dakwan Mai Na Najeriya

Amurka Ta Ƙwace Wani Babban Jirgin Dakwan Mai Na Najeriya

-

Dakarun tsaron gabar tekun Amurka da ke aiki tare da sojojin ruwan ƙasar, sun kama wani babban jirgin ruwa na Najeriya da ake kira da Skipper, sakamakon yadda ake zargin ana amfani da jirgin wajen satar danyen mai da fashin teku da dai sauran laifukan da suka shafi ƙasa da ƙasa.

 

A cewar jami’an tsaron Amurka, sun kama jirgin ruwan ne a lokacin da suke aiwatar da wani aikin a ƙarƙashin dokar tabbatar da doka da oda ta ƙasar, wacce shugaba Donald Trump ya sanar.

 

Hukumomin sun bayyana cewa, a lokacin da aka kama jirgin ruwan na dakon mai, akwai tutar ƙasar Guyana a jikinsa.

 

Nigerian Post ta bibiyi cewa, sai dai sashen da ke kula da harkokin jiragen ruwan ƙasar ta Guyana, ya ce ko kaɗan jirgin baya da rijista da su, kuma yana amfani da tutar ƙasar ne ta haramtatciyar hanya.

 

Ita ma dai hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ruwa ta Najeriya ta bakin mai magana da yawunta Edward Osagie, ya ce basu da masani kan lamarin a hukumance.

 

Bayaga hukumar NIMASA, shima shugaban ƙungiyar masu jiragen ruwa ta Najeriya Otunba Sola Adewuni, ya ce baya da wasu gamsassun bayanai kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎‘Yanbindiga Sun Hallaka Mutane 20, Sun Kone Rabin Wani Gari a Katsina

Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a garin Doma, dake Karamar Hukumar Faskari, dake cikin Jihar Katsina, bayan da ’yan bindiga dauke da manyan...

Jami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu– Ministan Tsaro 

Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce jami’an sojojin da aka kama bisa zargin yunkurin juyin mulki da aka dakile sun san sakamakon abin da...

Most Popular