HomeSashen HausaKwamishinan ’Yansanda Ya Karɓi Baƙuncin Sabon Kwamandan Rundunar Sojin Saman Najeriya Da...

Kwamishinan ’Yansanda Ya Karɓi Baƙuncin Sabon Kwamandan Rundunar Sojin Saman Najeriya Da Aka Turo Katsina

-

Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Katsina, CP Bello Shehu, MNIM, ya karɓi bakuncin sabon Kwamandan da aka turo na Rundunar Sojin Sama ta Najeriya, 213 Forward Operating Base Katsina, a ziyarar girmamawa da ya kai masa a yau Laraba, 17 ga Disamba, 2025. Ziyarar ta kasance ne domin ƙarfafa haɗin gwiwa da fahimtar juna tsakanin hukumomin tsaro.

 

Nigerian Post ta bibiyi cewa, Kwamandan 213 FOB Katsina, Air Commodore C. E. Illoh, ya nuna godiyarsa bisa kyakkyawar tarba da aka yi masa a yayin ziyarar. Ya bayyana cewa ziyarar ta zo ne domin sanin shugabancin rundunar ’yan sanda a jihar tare da ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar da ake da ita tun farko.

 

Ya kuma nemi ƙarin goyon baya da haɗin kai domin cimma burin samar da Jihar Katsina mai aminci da tsaro.

 

A nasa jawabin, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Katsina, CP Bello Shehu, MNIM, ya yaba wa Kwamandan bisa ganin dacewar kai masa ziyara a ofishinsa. Ya amince da rawar da Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ke takawa wajen yaƙi da ayyukan ta’addanci da laifuka, tare da jaddada aniyarsa ta ƙarfafa kyakkyawar alaƙar aiki tsakanin hukumomin.

 

Bayanin hakan na kunshe acikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya fitar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

‎‘Yanbindiga Sun Hallaka Mutane 20, Sun Kone Rabin Wani Gari a Katsina

Aƙalla mutane 20 ne suka rasa rayukansu a garin Doma, dake Karamar Hukumar Faskari, dake cikin Jihar Katsina, bayan da ’yan bindiga dauke da manyan...

Jami’an da Aka Kama Kan Yunkurin Juyin Mulki Za Su Ɗanɗana Kuɗarsu– Ministan Tsaro 

Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya ce jami’an sojojin da aka kama bisa zargin yunkurin juyin mulki da aka dakile sun san sakamakon abin da...

Most Popular