HomeSashen HausaTrump Ya Janye Jakadan Amurka daga Nijeriya

Trump Ya Janye Jakadan Amurka daga Nijeriya

-

Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya bayar da umarnin janye jakadan ƙasar daga Najeriya, Richard Mills, a wani bangare na sauyin tsarin diflomasiyya da ya shafi sama da ƙasashe 20 a duniya.

Najeriya na cikin ƙasashe 15 na Afirka da abin ya shafa, tare da wasu ƙasashe irinsu Masar, Senegal, Rwanda, Uganda, Nijar da Kamaru. An kuma aiwatar da matakin a wasu ƙasashen Asiya, Turai da Amurka ta Tsakiya da Kudu.

Rahotanni sun nuna cewa dukkan jakadun da aka janye an nada su ne a zamanin tsohon shugaban Amurka, Joe Biden, kuma an sanar da su cewa wa’adin aikinsu zai ƙare a watan Janairu mai zuwa.

Richard Mills ya fara aiki a Najeriya a Mayu na bara, kuma janyewarsa na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar ɗan tangarda a dangantakar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Amurka, musamman kan batutuwan biza da tsaro, duk da ci gaba da tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

NSCDC Ta Tura Jami’ai 1,256 A Jihar Katsina, Don Kare Muhimman Kadarorin Kasa Da Ababen More Rayuwa

A wani mataki na musamman domin tabbatar da isasshen tsaro, Kwamandan NSCDC na Jihar Katsina, AD Moriki, ANIM, ya amince da tura jami’ai 1,256 domin...

‎‘Yansanda Sun Jaddada Ƙara Matakan Tsaro Yayin Bukukuwan Kirsimeti

‎Yayin da ‘yan Najeriya ke shirin shiga bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara, Shugaban Rundunar ‘Yan Sanda ta Ƙasa, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ya ba da...

Most Popular