HomeSashen HausaTrump Ya Janye Jakadan Amurka daga Nijeriya

Trump Ya Janye Jakadan Amurka daga Nijeriya

-

Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya bayar da umarnin janye jakadan ƙasar daga Najeriya, Richard Mills, a wani bangare na sauyin tsarin diflomasiyya da ya shafi sama da ƙasashe 20 a duniya.

Najeriya na cikin ƙasashe 15 na Afirka da abin ya shafa, tare da wasu ƙasashe irinsu Masar, Senegal, Rwanda, Uganda, Nijar da Kamaru. An kuma aiwatar da matakin a wasu ƙasashen Asiya, Turai da Amurka ta Tsakiya da Kudu.

Rahotanni sun nuna cewa dukkan jakadun da aka janye an nada su ne a zamanin tsohon shugaban Amurka, Joe Biden, kuma an sanar da su cewa wa’adin aikinsu zai ƙare a watan Janairu mai zuwa.

Richard Mills ya fara aiki a Najeriya a Mayu na bara, kuma janyewarsa na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar ɗan tangarda a dangantakar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Amurka, musamman kan batutuwan biza da tsaro, duk da ci gaba da tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina State Government To Reward Athletes Who Attaracts Medals To The State

The commissioner of sports and youth development Alh Aliyu Lawal Zakari Shargalle has reaffirm the state government commitment to reward any athlete who attracts medals...

CP Bello Shehu Deploys More Personnel to Rescue Kidnap Victims in Katsina Metropolis

Katsina State Police Command has confirmed the shooting of one person and kidnapping of three others in Katsina metropolis. This is contained in a statement issued...

Most Popular