HomeSashen HausaTrump Ya Janye Jakadan Amurka daga Nijeriya

Trump Ya Janye Jakadan Amurka daga Nijeriya

-

Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya bayar da umarnin janye jakadan ƙasar daga Najeriya, Richard Mills, a wani bangare na sauyin tsarin diflomasiyya da ya shafi sama da ƙasashe 20 a duniya.

Najeriya na cikin ƙasashe 15 na Afirka da abin ya shafa, tare da wasu ƙasashe irinsu Masar, Senegal, Rwanda, Uganda, Nijar da Kamaru. An kuma aiwatar da matakin a wasu ƙasashen Asiya, Turai da Amurka ta Tsakiya da Kudu.

Rahotanni sun nuna cewa dukkan jakadun da aka janye an nada su ne a zamanin tsohon shugaban Amurka, Joe Biden, kuma an sanar da su cewa wa’adin aikinsu zai ƙare a watan Janairu mai zuwa.

Richard Mills ya fara aiki a Najeriya a Mayu na bara, kuma janyewarsa na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar ɗan tangarda a dangantakar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Amurka, musamman kan batutuwan biza da tsaro, duk da ci gaba da tattaunawa tsakanin ɓangarorin biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Dalilan Da Ya Sa Na Bar APC Na Koma ADC– Inji Wada Protocol

‎Tsohon hadimin tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari, Alhaji Mustapha Abdu Saulawa, wanda aka fi sani da Wada Protocol, ya bayyana dalilin da...

Yaron Shago Ya Hallaka Ubangidansa da Almakashi a Gombe, Kwanaki Kadan Da Aurensa

Jihar Gombe ta shiga alhini biyo bayan wani mummunan lamari da ya faru a unguwar Bolari, cikin birnin Gombe, inda wani yaron shago ya kashe...

Most Popular