HomeSashen HausaDikko Radda Ya Amince Da Naɗin Sabbin Manyan Sakatarori a Jihar Katsina

Dikko Radda Ya Amince Da Naɗin Sabbin Manyan Sakatarori a Jihar Katsina

-

Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya amince da naɗin sabbin manyan sakatarorin jihar.

 

Gwamnan ya ce an gudanar da naɗin bi sa cancanta da sabbin manyan sakatarorin da aka naɗa suka nuna ta hanyar cin jarabawar da Cibiyar Ma’aikata ta Najeriya ta gudanar a madadin gwamnatin jihar Katsina.

 

Gwamnan wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan jihar Mallam Falalu Bawale, ya buƙaci waɗanda aka naɗan da su yi aiki da ƙwarewa tare da nuna ƙwazo.

 

Nigerian Post ta bibiyi cewa, sabbin manyan sakatarorin sun haɗa da Tukur Hassan Dan Ali, Junaidu Muntari da Yahaya Abdullahi.

 

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban sashen yaɗa labarai na shugaban ma’aikatan jihar Abubakar Yaro Bindawa ya fitar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Katsina Police Received 29 New ASPs From The Nigeria Police Academy, Wudil

The Katsina State Police Command has received 29 newly posted Assistant Superintendents of Police (ASPs) from the Nigeria Police Academy, Wudil. Welcoming the officers, the...

Yawancin Fulanin Da Suke Ta’addanci Ba Su Da Addini, Ba Su San Allah Ba– Nasir El Rufa’i ‎

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufa’i, ya bayyana cewa yawancin mutanen Fulani da ake zargi da aikata ta'addanci da kashe kashe a sassa daban...

Most Popular